Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Masarauta: Mun Dawo Daga Rakiyar Ganduje, Cewar Dan Gandujiyya

by
3 years ago
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Wani fitaccen dan Gandujiyya a jihar Kano mai suna Kwamred Jamilu Wahada ya bayyana cewa sun dawo daga rakiyar gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, a kan rikicin da ya ke yi da Masarautar Kano karkashin jagorancin Mai Martaba Muhammadu Sanusi II ne, saboda yadda rikicin ke dakile ayyukan cigaba da gwamnatin jihar ke gudanarwa.

Kwamred Wahada,  wanda ya yi kaurin suna wajen tallata siyasar Gwamna Ganduje a baya, ya bayyana haka ne a shafinsa na Facebook, ya na mai kira ga sauran ’yan uwansa ’yan Gandujiyya da su kaurace wa shiga wannan rikici, wanda ya ke yin illa ga cigaban jihar.

Idan za a iya tunawa, a kwanakin baya ne gwamnatin jihar ta kekketa Masarautar Kano zuwa gida biyar, inda ta kirkiri masarautu hudu a wani yanayi da a ke kallo na yunkurin rage wa Sarkin Kano ikon fada a ji a fadin jihar.

Labarai Masu Nasaba

Birtaniya Ta Kwato Dala Miliyan 23 Da Ake Zargin Marigayi Abacha Ya Sha Kwana Da Su

Barazanar Da Kilisar Matasa Ke Ci Gaba Da Yi A Kano

Haka nan kuma hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar ta dawo da binciken da ta fara yi wa sarkin kan zargin ta’annati da dukiyar masarautar. To, amma masu lura da al’amuran yau da kullum na kallon binciken a matsayin bi-ta-da-kullin siyasa.

Wahada ya ce, tun daga lokacin da a ka fara rikicin, hankalin kowa ya karkata kan rigimar, inda hatta gwamnatin jihar ta bige ta tattalin rigima maimakon mayar da kai ga ayyukan alheri.

Ya ce, “ni Comrade Jamilu Wahada ni dan jam’iyyar APC ne kuma ni dan Gandujiyya ne cikakke (amma) daga yau ku sani cewa, Ina tare da Mai martaba Sarkin Kano Muhamamdu Sanusi II dari bisa dari.”

Ya cigaba da cewa, “Ina kira ga gwamnatin Kano cewa wajibi ne ta taimaki ‘yan jam’iyya wadanda su ka sha wahala a unguwanninsu a lokacin zabe, amma ta ki ta maida hankali a kan rihima da Masarautar Kano, domin a kautar da hankalin ‘yan jam’iyya da mu ka wahala a mazabarmu.”

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Za A Yi Waje Da Bakin Haure Masu Yawa Daga Cikin Najeriya

Next Post

Shawarar Malam Abdulkarim Ga Matan Aure: Ku Saki Bokaye, Ku Kyautata Mu’amula Da mazajenku

Labarai Masu Nasaba

Birtaniya Ta Kwato Dala Miliyan 23 Da Ake Zargin Marigayi Abacha Ya Sha Kwana Da Su

Birtaniya Ta Kwato Dala Miliyan 23 Da Ake Zargin Marigayi Abacha Ya Sha Kwana Da Su

by Leadership Hausa
1 week ago
0

...

Kilisa

Barazanar Da Kilisar Matasa Ke Ci Gaba Da Yi A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 weeks ago
0

...

NSCDC

‘Yansanda Sun Lakada Wa Kwamadan NSCDC Na Jihar Imo Duka

by Khalid Idris Doya
3 weeks ago
0

...

Bana

A Shirye-shiryen Karamar Sallar Bana…

by Abdullahi Muh'd Sheka and Bello Hamza
3 weeks ago
0

...

Next Post
Haramun Ne Namiji Ya Taya Matarsa Aiki A Kabilar Goroka

Shawarar Malam Abdulkarim Ga Matan Aure: Ku Saki Bokaye, Ku Kyautata Mu’amula Da mazajenku

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: