Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Karyata Bacewar Sojinta 23 Da Manyan Motocinta 8

by
4 years ago
in LABARAI, MANYAN LABARAI
1 min read
Sojoji sun Musanta Batan Jami’an Su
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Kwamandan Rundunar, ‘Operation Lafiya Dole,’ rundunar da ke fafatawa da ‘yan ta’adda a yankunan Arewa maso gabashin kasarnan, ya karyata rahotannin da ke nu ni da bacewar Sojojin rundunar 23 gami da manyan motocin rundunar 8.

Manjo Janar Nicholas Rogers, ya shaida wa gidan talabijin na ‘Channels,’ ranar Litinin cewa, sam babu ma wani rahoton yi wa rundunar wani kwantan bauna, Sojojin dai suna gudanar da ayyukansu ne kamar yadda suka saba a yankunan na Kwakwa da Bula Naglin, na Jihar ta Borno.

Ya bayyana cewa, a lokacin da suke gudanar da aikin nasu ne wasu daga cikin motocin nasu suka gaza saboda rashin kyawun hanya, wanda a lokacin ne ‘yan ta’addan suka kawo wa Sojojin hare-hare har sau biyu, kuma duk Sojojin suna kora su tare da agajin mayakan Sojin ta sama.

Labarai Masu Nasaba

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

Ya bayyana cewa a hakan ne aka ji wa wani babban jami’in rundunar da kuma wani Soja guda ciwo, amma sun kashe sama da maharan ‘yan ta’addan na Boko Haran 22 a lokacin fafatawan. Yayin kuma da aka kwaso motocin da suka gazan aka kuma kai karin dakarun Soji.

A karshen mako ne dai wasu kafafen yada labarai suka watsa rahotannin da ke cewa, akalla Sojin Nijeriya 23 ne suka bata, bayan wani kwantan bauna da maharan ‘yan ta’addan Boko Haram suka yi masu a kauyan Boboshe, da ke karamar hukumar Bama, ta Jihar Borno.

Aka ce kuma takwas daga cikin manyan motocin sojan 11 da aka tura domin su kawar da ‘yan ta’addan sun bace bayan harin na kwantan bauna a ranar ta Asabar.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Rundunar Soji Ta Musanta Kashe Sojoji A Adamawa

Next Post

An Sake Kashe Wani Dan Nijeriya A Kasar Afrika Ta Kudu

Labarai Masu Nasaba

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

by Abubakar Abba
2 hours ago
0

...

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

by
6 hours ago
0

...

Mutum 5 Sun Mutu Kan Rikicin ‘Yan Kasuwa Da ‘Yan Babura A Abuja

Mutum 5 Sun Mutu Kan Rikicin ‘Yan Kasuwa Da ‘Yan Babura A Abuja

by
7 hours ago
0

...

Ministar Kudi Ta Dakatar Da AKanta Janar Na Kasa Kan Zargin Badakalar Biliyan 80

Ministar Kudi Ta Dakatar Da AKanta Janar Na Kasa Kan Zargin Badakalar Biliyan 80

by
8 hours ago
0

...

Next Post

An Sake Kashe Wani Dan Nijeriya A Kasar Afrika Ta Kudu

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: