Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Rundunar ‘Yan Sanda Ta Kama Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 20 A Legas

by Tayo Adelaja
October 7, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Wakilinmu

Rundunar ‘yan sandan ta jihar Legas ta kama Tabar Wiwi da kuma wasu mugayen ƙwayoyin masu tsada da aka ƙiyasta kuɗin su ya kai sama da naira miliyan 20.

An kama Tabar ce, a wani samame da ‘yan sanda suka kai a wata maɓoyar ɓata gari da ke unguwar Itire a Mushin, inda aka samu Tabar a cikin Buhunhuna 38.

Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Edgal Imohimi wanda ya bayyana hakan a taron manema labarai ya ce, an kuma kama waɗanda ake zargi su 52 lokacin da aka kai samamen.

Edgal ya ƙara da cewa an samu wanna nasarar ne sakamakon haɗin gwiwa tsakanin rundunar ‘yan sanda tare da haɗin gwiwar alummar jihar da suke da ƙyaƙƙyawat alaƙa tun da daɗewa, mazauna yankin da abin ya auku ne suka sanar da jami’anmu  wannan maɓoya ta ɓata garin.

Ya ci gaba da cewa, a bisa bayanan da muka samu, ɓata garin sun jima suna cin Karen su ba babbaka a yankin, suna aikata ta’asa, inda ya bada umarnin da akai samamen da daddare don kama ɓata garin har aka samu nasarar kama maza 44 da mata 8 tare da kuma buhun Tabar  Wiwi 38.

Kwamishinan ya ce, an kuma kama waɗanda ake zargin da wasu mugayen ƙwayoyi da aka yi masu laƙabi da ‘’Bible’’, inda ya ja hankalin al’ummar jihar da su farga da irin waɗannan mugayen ƙwayoyi.

Sannan ya yi kira ga al’ummar jihar ta Legas da su sa ido akan mugayen ƙwayoyin don gudun kada a sayarwa ‘ya ‘yansu,  saboda hakan na iya haifar da wasu illoli.

A cewar kwamishinan,  ya lura da alaƙar da  miyagun ƙwayoyi da  yawan aikata manyan laifufuka yasa muka haɗa gwiwa tsakanin mu da Hukumar Hana Sha da fataucinmiyagun kwayoyi watau (NDLEA) da kuma sauran jami’an tsaro don yaki da shaye-shaye a ɗaukacin faɗin jihar Legas da kewaye.

Mista Edgal, ya bayyana jin daɗinsa akan haɗin kan da al’ummar jihar suke baiwa rundunar, kuma za su cigaba da yin iyakar ƙoƙarinsu don bankaɗo dukkkan maɓoyar ɓata gari da ke cikin jihar  ta Legas.

SendShareTweetShare
Previous Post

Wutar Lantarki Ta Yi Ta’adi A Gidan Rediyon Kwalejin ATAP

Next Post

LEADERSHIP Na Taka Rawar Gani Ga Jami’an Tsaro —Kwamishinan ‘Yan Sanda

RelatedPosts

Hijira

Zulum Ya Bankado ’Yan Hijira 650 Na Bogi

by Muhammad
12 hours ago
0

Ya Sake Koma Wa Dikwa Bayan Harin Boko Haram Daga...

Allurar Rigakafin

An Fara Yin Allurar Riga-kafin Korona a Nijeriya

by Muhammad
3 days ago
0

Yau Ake Sa Ran Buhari Da Osinbajo Za Su Karbi...

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
2 weeks ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Next Post

LEADERSHIP Na Taka Rawar Gani Ga Jami’an Tsaro —Kwamishinan ‘Yan Sanda

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version