Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Kame Dan Bindigar Da Ya Kashe Dan Kasar Jamus

by Muhammad
December 26, 2020
in RAHOTANNI
2 min read
Jamus
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kano

Rundunar ‘Yan Sanda jihar Kano ta bayyana kama Abubakar Isma’il mai shekara 30 da haihuwa wanda ake zargi da kashe  jami’in dan sanda daya  da kuma yin garkukwa da wani baturen kasar Jamus  mai suna Kreser Michael, ma’aikacin kamfanin Dantata & Sawoe a Kano.

samndaads

Idan za’a tuna  a ranar 16 ga watan aprilun shekara ta 2018  wasu ‘yan bindiga suka sace injiniyan dan kasar Jamus bayan sun kashe dan sandan dake aiki tare dashi  a wurin da suke aikin  titin zuwa Karamar Hukumar Madobi a Kano.

Kakakin rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Abdullahi Haruna Kiyawa  ya bayyanawa manema labarai cewa an kama Isma’il  ne a ranar 19 ga watan disambar shekara ta 2020 bayan watannin talatin da faruwar al’amarin.

Hakazalika wanda ake zargin ya amsa cewa sune suke kai hare hare  a yakin Kananan Hukumomin Rimin Gado, Gwarzo, Karaye, Kiru, Bebeji da Tudun Wada duk a Jihar Kano da wasu makwabtan jihohi da suka hada da Kaduna da Katsina tsawon shekara biyar.

Haka kuma ya ambata sunayen wadanda ke cikin wannan tawaga tasu da suke aikata irin wannan ta’addaccin. ‘Yan sanda na kara zurfafa bincike  domin damko sauran wadanda ake zargin” inji shi.

A wani cigaban rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta samu nasarar damke wani mutun mai suna Salmanu Muhammad dake unguwar Gwammaja  wanda ake zargi da karya wani wurin ajiyar kaya dake unguwar Tal’udu a kwaryar birnin Kano.

Wanda ake zargin Salmanu Muhammad a cewar kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Kano Abdullahi Kiyawa yace an kama Salmannu ne a ranar 27 ga watan Nuwambar shekara ta 2020 tare da wata mota kirar Pick –up makare da kayan gini da kujeru na sata wanda aka kiyasata kudinsu ya tasamma Naira Miliyon takwas.

Dakarun ‘yan sanda ne suka damke motar da kuma Salmanu Muhammad  Bashir mai shekata 36 dake unguwar Gwammaja a Jihar Kano.  Kuma wanda ake zargin ya amsa  laifin karya wurin ajiyar kayan dake unguwar Tal’udu a Kano.

Salmanu Muhammad ya bayyana yadda ya lalata makullin kofar sannan ya maye gurbinsa  da wani sabo iri guda da wanda ya lalalta kuma ya kwashi kayan sama da Naira Miliyon takwas. An gano Mamallakin wurin ajiyar kuma ana ci gaba da gudanar da bincike. In ji Kiyawa

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda  Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Garkuwa Da Mutane A Zamfara

Next Post

Shugaban Majalisar Dattawa Ya Taya Kiristoci murnar kirsimeti

RelatedPosts

Kasuwar Mile 12

Kwamitin Da Shugaban Kasuwar Mile 12 Ya Nada Na Cigaba Da Jajanta Wa Manoman Arewacin Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
5 mins ago
0

Sabon kwamitin da Babban Shugaban kasuwar mile 12 Intanashinal market...

Sojoji Sun Farmaki Mahakar Ma’adanai A Zamfara, Sun Cafke ‘Yan Bindiga 150

Ranar Mazan Jiya: Babu Wani Abin Murna Ga Tabarabrewar Tsaro – Dattawa Ga Buhari

by Sulaiman Ibrahim
9 mins ago
0

Dattawan Nijeriya a karkashin inuwar gamayyar kungiyar wato (COPANE), sun...

DATA

Har Yanzu Ana Sayar Da (DATA) Kan Tsohon Farashi Duk Da Ragin Kashi 50

by Sulaiman Ibrahim
24 hours ago
0

Yawancin masu amfani da layin sadarwa sun ce har yanzu...

Next Post
Dattawa

Shugaban Majalisar Dattawa Ya Taya Kiristoci murnar kirsimeti

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version