Rundunar 'Yansanda Ta Shelanta Neman Dakta Idris Dutsen Tanshi Ruwa A Jallo
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rundunar ‘Yansanda Ta Shelanta Neman Dakta Idris Dutsen Tanshi Ruwa A Jallo

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Dutsen Tanshi

Rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ta ayyana neman fitaccen malamin addinin musulunci a jihar, Imam Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi ruwa a jallo bisa zarginsa da kin mutunta kotu.

Kuma an sanya tukuici mai gwabi ga duk wanda ya tona inda malamin yake boye a halin yanzu.

  • Guterres Ya Gabatar Da Sakon Murnar Sabuwar Shekara Ta Kasar Sin
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Tarayya Ta Kayyade Farashin Kayayyaki Cikin Kwanaki 7

‘Yansanda a wata shelar musamman da ta fitar a ranar Alhamis ta ce, umarnin ya fito ne daga ofishin sufeto-janar na hukumar, inda suka roki dukkanin wani ko wasu da ke da bayanin yadda za a kama Idris da ya gaggauta sanar da jami’in ‘yansanda mafi kusa da shi.

Sanarwar ta ce Idris da ake nema ruwa a jallo sama ko kasa na da shekaru 62 a duniya, kuma an masa gani na karshe ne a adireshin Dutsen Tanshi da ke Bauchi amma yanzu ba a san inda yake ba.

“Da zarar ka ganshi, kama shi ka mikashi ga caji ofis din ‘yansanda mafi kusa da kai ko kai tsaye zuwa ofishin mataimakin kwamishinan ‘yansanda, shafin binciken manyan laifuka na rundunar ‘yansandan jihar Bauchi ko a kira lambobin waya; 08151849417, 09048226246.”

Rundunar ta ce akwai tukuici ga duk wanda ya taimaka musu suka cafke malamin.

Idan za a tuna dai babban kotun shari’a mai lamba 1 da ke Bauchi ta bai wa ‘yansanda umarnin cafko malamin gami da gurfanar da shi a gabanta bisa zargin da kin mutunta gayyatar da kotun ta masa domin cigaba da sauraron karar da ake masa kan tada zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiya a jihar Bauchi.

Malamin dai ya yi abun da ya kira ‘Hijira’ ne bayan da hadakar jami’an tsaro suka yi wa gidansa kawanya da nufin kama shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar Sabuwar Shekarar Gargajiya Ga Al’ummar Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Gaisuwar Sabuwar Shekarar Gargajiya Ga Al’ummar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version