Abdullahi Muhammad Sheka">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Saboda Barazanar Tsaro Muka Sayar Da Tsohon Gidan Rediyon Manoma – Gwamnatin Kano

by Abdullahi Muhammad Sheka
January 29, 2021
in LABARAI
2 min read
Kananan Hukumomin Jihar Kano
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa, ta yanka filotai a Gidan Rediyon Manoma na Jihar Kano da ke Unguwar Tukuntawa ne sakamakon barazanar tsaro da gidan rediyon ke yi ga al’ummar da ke kewayansa.
Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano, Malam Muhammad Garba ne ya bayyana haka, yayin tattaunawarsa da manema labarai a Kano.

Muhammad Garaba ya ce, tun a shekarar 2010 aka daina amfani da wannan gidan rediyo, sakamakon bude makamancinsa da aka yi a garin Jogana. Ya kara da cewa, gwamnati ta so ta yi gidan rediyon manoma a wannan wuri, amma sakamakon tsofaffin kayan aiki da gurin ke da shi sai aka mayar da shirin manoman zuwa gidan rediyon Kano na Bello Dandago.

Ya ce, ko a ‘yan kwanakin da suka gabata, sun samu rahotannin da ke cewa an samu gawarwaki har guda uku a cikin Gidan Rediyon. Hakan yasa Gwamnati ta duba tare da ganin cewa bai kamata a bar filin a haka ya zama matattarar ‘yan iska ba.

“Duk wanda yake wannan wuri ya san fili ne na gwamnati, sannan a lokacin Marigayi Kabo Idris Shugaban Gidan Rediyon Kano, ya ba da umarnin masu noma da ajiye ababen hawa su dena, amma aka kyale su. “Yanzu lokaci ya zo, saboda barazanar tsaro da mugan abubuwan da ake yi a gurin yasa gwamnati ta yanka gurin,” a cewar tasa.

Ya kara da cewa, ba dole ne sai gwamnati ta tuntubi wasu ba, idan har za ta saida wani guri da yake mallakinta. Ya ce, gwamnati za ta sanar da mutane ne kawai idan har gurin da take so ba mallakinta ba ne.

SendShareTweetShare
Previous Post

Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Umurnin Kotu Na Yashe Asusun Tsohon Gwamna Yari

Next Post

Kudirin Dokar Fetur: Yadda Kabilun Neja Delta Suka Dambace A Majalisar Wakilai

RelatedPosts

Garkuwa

An Kama Sojan Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Kayan Sojoji A Zamfara

by Abdullahi Muhammad Sheka
15 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim "An kama wani jami’in soja da budurwarsa...

Aikin Wutar Mambilla  A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

Aikin Wutar Mambilla A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

by Abdullahi Muhammad Sheka
18 hours ago
0

Kungiyar gwamnonin arewa maso gabas sun nuna rashin jin dadin...

Bindiga

Gwamna Ortom Ya Yabawa Umarnin Buhari Na Hana Mallakar  AK47 Ba Bisa Ka’ida Ba

by Abdullahi Muhammad Sheka
19 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Gwamnan Jihar Benue Samuel Ortom a ranar...

Next Post
Kudirin Dokar Fetur: Yadda Kabilun Neja Delta Suka Dambace A Majalisar Wakilai

Kudirin Dokar Fetur: Yadda Kabilun Neja Delta Suka Dambace A Majalisar Wakilai

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version