Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda  Ya Yi Alkawarin Kawo Karshen Garkuwa Da Mutane A Zamfara

by Muhammad
December 26, 2020
in RAHOTANNI
2 min read
Jigawa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Hussaini Yero Zamfara,

Sabon kwamishinan ‘yan sanda na  jihar Zamfara, Alhaji Abutu Yaro, ya dau alkawarin kawo karshen ‘yan bindiga da masu satar mutane wadanda suka gurgunta ci gaban tattalin arzikin jihar.

samndaads

Kwamishina Abutu Yero, ya bayyana haka ne a loakcin da yake zantawa da manema labarai a Hedikwatar ‘yan sandan da ke Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

Kwamishinann ya kara da cewa,’Game da kalubalen tsaro a jihar wadanda suka hada da satar shanu da ‘yan fashi da makami da kai harin ramuwar gayya da satar mutane da kisan gilla da rikicin manoma da makiyaya, ya tsara yadda za a magance matsalar wadannan kalubana da suka addabi jihar.’ In ji Abutu Yaro.

Haka kazalika, jajircewa da kuma sadaukar da kai musamman ga masu munanan laifuka tare da hadin gwiwa da Gwamnatin Jiha, Sarakunan Gargajiya, Al’umma da shugabannin addinai zai taimaka wajan samun dawamamen zaman kafiya.

Kwamishina ya jaddada cewa,dole ne ‘yan sanda su kasance masu himma, masu kariya ga al’umma da  warware matsaloli da tallafawa al’umma tare da basu tsaro a ko da yashe.

Ya tabbatar wa jama’a cewa ‘yan sanda karkashin kulawar sa za su sauke nauyin da ke kansu daidai da ka’idojin aikin rundunar.

Ya kuma yi gargadin cewa, ba za a amince da take hakki na dan adam ba, Kuma ba zamu aminta ta  amsar  cin hanci da rashawa da sauran halaye marasa kyauba.

Kwamishinan ya yi kira da a ci gaba da ba da goyon baya, hadin kai da hadin gwiwa ga kowa da kowa ta hanyar ba da bayanai masu amfani ga ‘yan sanda kan ayyukan masu aikata laifuka don daukar matakin gaggawa akan su.

SendShareTweetShare
Previous Post

Jami’o’in Nijeriya Ba Su Mayar Da Hankali Wajen Gudanar Da Bincike  Masana

Next Post

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Kame Dan Bindigar Da Ya Kashe Dan Kasar Jamus

RelatedPosts

Alaba

‘Yan Kasuwan Arewa A Legas Mu Hada Kai Don Cigaba – Muhammadu Alaba

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Hadin kai shi wani babban al’amari...

Jama'a

Taimaka Wa Jama’a Shi Ne Shugabanci Nagari -Matawalle Alagwadun Legas  

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai,   Matawallen Alagbado, Alhaji Muhammadu ya...

Samarun

Yadda Rasuwar Matashi Ta Jefa Mutane Cikin Alhini A Samarun Zariya

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Idris Umar, A ranar laraba ta wannan makon da...

Next Post
Jamus

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Kame Dan Bindigar Da Ya Kashe Dan Kasar Jamus

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version