Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Sake Gina Borno: Zulum Ya Gana Da Wakiliyar Tarayyar Turai A Abuja

by Muhammad
February 20, 2021
in LABARAI
1 min read
Tarayyar Turai
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela,

A fadi-tashin lalabo hanyoyin da za su taimaka wajen sake farfado da jihar Borno, a ranar Alhamis Gwamna Umara Zulum ya gana da sabuwar wakiliyar Tarayyar Turai a Nijeriya, Misis Cecile Tassin-Pelzer a Abuja.

A lokacin wannan ziyara a ofishin ta (EU House), Gwamna Zulum ya bukaci kungiyar Tarayyar Turai ta dauki matakan aiwatar da ingantattun kudurorin raya yankunan karkara a jihar Borno.

Har wala yau, Gwamnan ya gabatar wa da wakiliyar Tarayyar Turan bukatar neman karin gudanar da ayyukan ci gaban jihar, tare da yaba mata dangane da ci gaba da goyon bayan da ta ke bai wa jihar.

 

Haka kuma, Zulum ya ankarar da EU wajen sanya ido a gudanar da wasu muhimman ayyukan ci gaba na hadin gwiwa da kungiyoyin bayar da agaji ke aiwatarwa a jihar. Haka kuma ya taya babban jami’in murnar kasancewa wakili a Nijeriya tare da bashi tabbacin samun goyon baya.

 

“Wanda tun a lokacin da nake kwamishina, ina da kyakkyawar alaka tsakanina da Tarayyar Turai, kuma makasudin zuwa na shi ne taya ka murna zuwa Nijeriya.”

 

A nata jawabi, Misis Tassin-Pelzer ta bai wa Zulum tabbacin ci gaba da samun hadin kai da kyakkyawar alaka tsakanisu da gwamnatin jihar Borno.

 

Ta kuma kara bai wa Gwamna Zulum tabbacin cewa ta hanyar tarayyar Nijeriya za su ci gaba da bayar da fifiko wajen talkafa wa yan gudun hijira da aiwatar da shirye-shiryen ci gaban kasa.

 

Kafin nada ta wakiliya a Nijeriya, Misis Tassin-Pelzer ita ce wakiliyar Tarayyar Turai a kasar Senegal tsawon shekaru uku.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kwara Ta Rufe Makarantu 10 Kan Rikicin Hijabi  

Next Post

Ana Iya Yanke Mani Guiwa Idan Ban Samu Beli Ba – Maina

RelatedPosts

Dabbobi

Zamanin Kiwon Dabbobi A Sake Ya Shude – ACF

by Muhammad
5 hours ago
0

Kungiyar Ta Goyi Bayan Matsayin Gwamnonin Arewa Daga Abubakar Abba,...

Garkuwa

Neja Ce Kan Gaba Wajen Fuskantar Matsalar Masu Garkuwa Da Jama’a- Gwamna Bello  

by Muhammad
5 hours ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, Gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello ya...

Barista

Barista Ahmad Ghazali Ya Zama Abin Koyi -Mansur Dandago

by Muhammad
6 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Watan Azumi na cikin lokutan da...

Next Post
Maina

Ana Iya Yanke Mani Guiwa Idan Ban Samu Beli Ba – Maina

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version