Da yake jawabi a wajen wata gasar musabakar Alkur’ani mai girma a birnin Sakkwato ranar Lahadi, Sultan Saad Abubakar, ya ce, “abin damuwa ne matuka” ganin irin yadda shafukan sada zumunta kamar su Facebook da Whatsapp da Instagram da 2go ke dauke wa yara hankali daga karatunsu.
Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ya ambato shi yana cewa ya kamata iyaye su rinka kula da yaransu.
”Irin yadda ‘yan mata ke bata mafi yawan lokutansu a kan shafukan sada zumunta abin damuwa ne kuma wannan yana da hadari ga al’ummarmu.
Ya yi kira ga iyaye da su tabbatar da cewa ‘ya’yansu mata sun yi amfani da lokacinsu wajen yin abubuwa masu ma’ana da rayuwa, ciki har da karatun Alkur’ani, domin yin hakan ne zai sa su zamo iyaye na-gari”.