Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

byCGTN Hausa and Sulaiman
12 months ago
Sin

Ga duk mai bibiyar ci gaban da kasar Sin ta samu musamman a gwamman shekarun da suka gabata, tilas ya amince cewa salon da kasar ke bi wajen zamanantar da kai ya ciri tuta, duba da yadda ya haifarwa ’yan kasar da mai ido ta fuskar tsame alumma daga kangin talauci, da samarwa alummar Sinawa damar more ababen more rayuwa masu inganci, da raya fasahohin zamani da sauransu, wadanda dukkanin su ke zama muhimmin misali mai kima ga sauran kasashe masu tasowa musamman na Afirka.

 

Kasashen Afirka na iya koyi da dabarun kasar Sin ta fuskar aiwatar da managartan manufofin raya kai, da gudanar da sauye-sauye da zamanantarwa, ta yadda su ma za su daga matsayin su daga kasashen da alummun suke fama da karancin karfin tattalin arziki zuwa cibiyoyin raya tattalin arziki a matakin kasa da kasa.

  • Xi Ya Mika Gaisuwar Ban Girma Ga Dattawa A Jajibirin Ranar Tsofaffin Kasar Sin
  • Ban Yi Nadamar Yakar PDP A Zaben 2023 Ba – Wike

Mun dai ga misalan hakan a bangaren kasar Sin, wadda ta kawar da fatara, da cike gibi tsakanin mawadata da masu rauni, zuwa wanzar da ci gaba mai dorewa a dukkanin fannoni, matakan da suka kai kasar zuwa turbar samun ci gaba a dukkanin bangarori, da daidaita tafiya tsakanin raya tattalin arzikin kasa da ci gaban zamantakewa da walwalar alumma.

 

A daya hannun, muna iya cewa yadda kasashen Afirka ke kara rungumar tafiyar samar da ci gaba tare da kasar Sin, karkashin tsare-tsare, da dandaloli daban daban abun a yaba ne. A duk inda muka duba muna iya ganin ayyukan hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka na raba ababen more rayuwa, da musayar kwarewa, da musayar aladu, da karfafa kawance, da bunkasa cinikayyar hajoji da hidimomi tsakanin sassan biyu.

 

Baya ga hakan, wasu karin sassa da ya kamata sassan biyu su inganta hadin gwiwa su ne batun samar da ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da kare muhallin halittu, da rage tasirin dumamar yanayi, da raya samar da makamashi mai tsafta, fannonin da tuni kasar Sin ta yi nisa a fannin cimma nasarar su.

 

Yayin da ake duba yiwuwar fadada kawance, da cudanya tsakanin Sin da kasashen Afirka a dukkanin fannoni, wajibi ne a jinjinawa yadda Sin din ke fadada tallafin da take baiwa kasashen Afirka ta fuskoki da dama, kamar samar da yankunan raya masanaantu, da yankunan cinikayya maras shinge, da taimakon raya fasahohin noma na zamani da dai sauran su.

 

Kaza lika, ya zama dole a yabawa kasar Sin don gane da sabbin shirye-shiryen hadin gwiwa 10 da ta gabatar a baya bayan nan, don ingiza zamanantar da kasashen Afirka abokan tafiyarta, shirye-shiryen da ko shakka babu za su yaukaka dunkulewar ayyukan hadin kan sassan biyu, kana sun dace da ajandar raya nahiyar Afirka ta nan zuwa shekarar 2063, da ma ajandar raya yankin cinikayya maras shinge na daukacin kasahen Afirka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

Babu Hannun Mijina A Wahalar Da Ƴan Nijeriya Ke Sha

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version