Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

Sama Da Dalibai 25 Suka Samu Haddar Alkur’ani A Makarantar Nurun Nabiyi

by Muhammad
December 29, 2020
in JAKAR MAGORI
1 min read
Dalibai
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka,

 

samndaads

A bikini saukar Alkur’ani Karo na goma na makaranatar Nurun Nabiyi dake Sabuwar Unguwa a Karamar Hukumar Kumbotso inda dalibai 70 suka Yi dacen Sauke Alkur’ani Mai girma, sannan Dalabai 25 daga cikin wancan adadi suka samu Haddar Alkur’ani Kamilan.

Shugaban makarantar Gwani Abdussalam Abdulkadir ne ya bayyana haka Alokacin da yake gabatar da jawabinsa. Bayan tabo dogon tarihin Makarantar, ya bayyana farin cikinsa bisa yadda a tsakanin shekara goma Dalabai sama da 360 makaranatar tayi bikin shaida saukar su tare da samun Hafizan Alkur’ani masu yawa daga cikin wannan adadi.

Da ya ke gabatar da jawabinsa Alhaji Abdullahi Namama Dan Majen San Turakin Ringim ya jinjinawa kokarin malaman wannan Makaranta Wanda yace duk nasarar da aka samu ta biyo bayan sadaukar da  kansu ne. Don Haka sai ya jakunnen dalban da suka samu wannan baiwa daga da cewa su dauka yanzu suka fara neman ilimi.

Alhaji Namama ya jadadda aniyarsa na ci gaba tallafawa irin harka ta Alkur’ani aduk inda aka bukaci hakan, daga Nan sai ya bukaci al’umma su kara jajircewa wajen gudanar da addu’o’in neman dorewar zaman lafiya a Jihar Kano da Kasa baki daya.

Shi ma a nasa jawabin, Dallatun Kano, Alhaji Bashir Mahe Alu Wanda shima Tsohon dalibin wannan Makaranta ne, ya bayyana farin cikinsa bisa ganin wannan muhimmiyar rana, daganan sai ya taya daliban da suka sauke Alkur’anin murnar wannan abin alhairi.

Cikin wadanda suka gabatar da jawabai alokacin bikin saukar, akwai Gwani Yusif Isyaka Rabiu, Sakataren ilimin Karamar Hukumar Kumbotso Alhaji Hussaini Baba da sauransu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Artabun ’Yan Kungiyar Asiri Ya Ci Rayukan Mutum Biyar A Bayelsa

Next Post

Ciwon Sanyin Mata (Sanyin Gaba) 2

RelatedPosts

Kotu Ta Yanke Wa Madamfari Zaman Kurkuku Na Shekara 10

Kotu Ta Yanke Wa Madamfari Zaman Kurkuku Na Shekara 10

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

Mai Shari'a Darius Khobo na babbar kotun jihar Kaduna, a...

An Gano Dangin Da Ba Su Da Zanen Tambarin Yatsu

An Gano Dangin Da Ba Su Da Zanen Tambarin Yatsu

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

A zamanin yanzu a duniya da ake amfanin da zanen...

An Cafke Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Damfara

An Cafke Dan Nijeriya A Indiya Da Laifin Damfara

by Sulaiman Ibrahim
2 hours ago
0

A ranar Larabar makon da ta gabata ne ‘yan sanda...

Next Post
Sanyin Gaba

Ciwon Sanyin Mata (Sanyin Gaba) 2

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version