Sama Da Mutum 150 Ke Hannun 'Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sama Da Mutum 150 Ke Hannun ‘Yan Bindiga A Jibiya – Shugaban Karamar Hukumar

byEl-Zaharadeen Umar
3 years ago
Jibiya

A halin da ake ciki kuma, shugaban karamar hukumar Jibiya a jihar Katsina Hon. Bishir Sabiu Maitan ya bayyana cewa akwai fiye da mutane 150 da ke rike a hannun masu garkuwa da mutane domin neman kudin fansa a karamar hukumar Jibiya.

Hon. Maitan ya yi wannan bayani ne a lokacin da yake yi wa wakilan kafafen yada labarai bayani irin kokarin da gwamnatin jihar Katsina karkashin jagorancin Aminu Bello Masari akan ‘yan gudun hijira da ke makarantar ‘yan mata da GGSS Jibiya.

  • Hare-Haren ‘Yan Bindiga Ya Tilasta Yara 3,000 Daina Zuwa Makaranta A Katsina

Shugaban ya kara da cewa kullum sai an kai hari a karamar hukumar Jibiya kuma kullum sai an dauki mutane da niyyar a biya kudin fansa kafin a sake su.

”Wannan al’amarin ya wuce duk inda ake tunanin sa, kusan yanzu na koma ba ni da wani aiki da wuce kula da ‘yan gudun hijira da kuma karbar rahotanni na kai hare-haren wuce gona da iri daga ‘yan bindiga, kullum maganar ke nan.”in ji shi.
Ya nunar da cewa yanzu haka akwai mutum 60 dukkansu ‘yan gari daya suna hannun ‘yan bindiga ana ta kokarin ganin yadda za a kubutar da su daga hannun masu garkuwa da mutane sai an ba da kudin fansa.

A cewarsa, “jami’an tsaro da kuma ita kanta gwamnati suna kokari sosai wajan ganin an kawo karshen wannan al’amari, amma fa idan an toshe can, sai can ya bude, Allah ya Kawo mana zaman lafiya,” in ji shi.

Shugaban karamar hukumar dai ya ce wannan adadin da ya ambata an dauke mutanen ne a cikin wata guda kacal, sannan ya kara da cewa a haka ma an sako wasu da iyalansu da suka biya kudin fansa.

Karamar Hukumar Jibiya dai tana cikin kananan hukumomin da ‘yan bindiga suka hana sakat, inda yanzu haka fiye da mutum 20,000 na gudun hijira, wasu a Nijeriya wasu kuma a jamhuriyar Nijer.

Haka kuma aikin ‘yan bindigar ya tilasta wa da yawa daga cikin magidanta tserewa su bar iyalan su, wasu kuma tuni suka riga mu gidan gaskiya, amma babar matsalar ita ce yadda wannan al’amari ya ki ci ya ki cinyewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Richarlison Ya Kammala Komawa Tottenham

Richarlison Ya Kammala Komawa Tottenham

LABARAI MASU NASABA

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version