Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

An Samar Da Shirin Bai Wa Ma’aikata Abincin Rana Kyauta A Nasarawa

by Tayo Adelaja
September 21, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abdullahi, Lafia

Kwamishinan ma’aikatar ilimin musamman, kimiya da fasaha ta Jihar Nasarawa Farfesa Jonathan Ayuba, ya kirkiro da kuma soma aiwatar da shirin bayar da abincin rana kyauta ga dukkanin wadanda ke aiki a ma’aikatar domin karfafa wa ma’aikatansa gwiwar aiki.

samndaads

Kwamishinan wanda ya bayyana haka ga manema labarai a garin Lafia ya ce, za a rika bai wa kowane ma’aikacin ma’aikatar abincin rana kyauta na kwanaki uku a tsakanin ranakun aiki.

A cewarsa,  daga yanzu a kashin kansa zai rinka bada abincin rana kyauta ga ma’aikatansa a ranakun Litinin da Laraba da kuma Juma’a a kowane mako.

Ta kwamishinan, “Dalilin samar da shirin shi ne, domin kara tabbattar da ma’aikatan ma’aikatar sun kasance tsintsiya madaurinki daya da kuma samar da wani dandali na tattaunawa da juna kan batuttuwan da za su kawo cigaba a ma’aikatar ba tare da la’akari da bambancin da ke a tsakanin ma’aikatan ba”.

“Muna amfani da lokacin cin abincin rana mu tattauna tsakanin babban sakatare da daraktoci da masu shara da direbobi. Idan aka samu kyakkyawar yanayin aiki da dangantaka mai kyau a tsakanin ma’aikata, aiki zai kara inganta”, in ji shi.

Har wa yau  ya ce, an gyara da kuma inganta kayan aiki domin kara cusa wa ma’aikata sha’awar zuwa aiki. Dagan an, sai ya bayyana cewa gwamnati ta fara shirin daukar dalibai a makarantar nakasassu da ke Lafia da kuma malamai da za su karantar da su. Tare da cewa ayyukan gina makarantun nakasassu da a yankin Akwanga da Keffi sun yi nisa.

Ya bayyana cewa ilimin nakasassu a Jihar Nasarawa kyauta ne tun daga matakin firamari har zuwa makarantun gaba da sakandare, kuma da zarar sun kammala karatun gwamnati tana daukar su aiki.

A karshe, kwamishinan ya yi kira ga nakkasassu a jihar da su yi amfani da damar makarantunsu da gwamnatin jihar ta gina su nemi ilimi su kuma koyi sana’o’in hannun don amfanin rayuwarsu da kuma bunkasa tattallin arzikin jihar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kungiyar Matasan Funtuwa Ta Caccaki Wakilcin Sanata Abu Ibrahim

Next Post

ILIMI: KAFOBA Ce Jigon Samun Ci Gaba A Sakandiren Kafin-Maiyaki –Honorabul Yahaya

RelatedPosts

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

by Sulaiman Ibrahim
13 hours ago
0

Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin da aka diba wa ’yan...

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

by Sulaiman Ibrahim
13 hours ago
0

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, ayau Juma’a, ta ce shirin Gwamnatin...

Zakzaky

Matar Sheikh EL-Zakzaky Ta Kamu Da Korona, In Ji Danta

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Matar Shugaban Kungiyar Musulunci a Nijeriya...

Next Post

ILIMI: KAFOBA Ce Jigon Samun Ci Gaba A Sakandiren Kafin-Maiyaki –Honorabul Yahaya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version