Sanata Gaidam Ya Talllafa Wa Matasa 400 A Mazabarsa Da Kayan Sana'o'in Dogaro Da Kai A Yobe
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sanata Gaidam Ya Talllafa Wa Matasa 400 A Mazabarsa Da Kayan Sana’o’in Dogaro Da Kai A Yobe

byMuhammad Maitela
3 years ago
Gaidam

Tsohon Gwamnan jihar Yobe, kuma Sanata mai wakiltar shiyya ta daya (Zone A) a zauren majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Ibrahim Gaidam tare da hadin gwiwa da Hukumar bunkasa yankunan kan iyakoki ta kasa: Border Communities Development Agency (BCDA)- sun kaddamar da tallafin kayan kiwon Kifi da sana’o’in dogaro da Kai ga matasa da mata sama da 400.

Da ya ke kaddamar da raba tallafin babban dakin taron karamar hukumar Damaturu, a babban birnin jihar Yobe, ranar Asabar, Sanata Gaidam wanda Muhammad Kiwata ya wakilta ya ce wannan kokari domin tallafa wa al’ummar mazaba da kayan sana’o’i hadi da horar da mata da Matasa, suna daga cikin abubuwan da Sanata Gaidam ke yi don kawar da zaman kashe wando domin samar da sana’a don jama’a su dogara da kansu.

  • Yobe Ta Arewa: Machina Ya Sake Samun Nasara Yayin Da Kotu Ta Kori Karar Da Aka Sake Shigarwa A Kansa 

Gaidam ya ce ya zama wajibi a matsayin su na shugabannin al’umma su tashi tsaye wajen samarwa da mata da matasa ayyukan yi musamman sana’o’in dogaro da kai, bayar da horo tare da tallafa musu da abubuwan da za su fara sana’o’in a lokacin da suka kammala samun horon.

Ya ce, “Saboda haka ne, ta hanyar hadin gwiwar fadar shugaban kasa mu ka yi kokarin bayar da tallafin wadannan kayan fara sana’o’i ga matasanmu sama da 400; domin kiwon Kifi wanda hakan zai taimaka su tsaya da kafafunsu.”

A nashi bangaren, babban jami’in Hukumar BCDA, Mista Rotimi Taiwo ya bukaci matasan su yi amfani da kayan da aka raba musu ta hanyar da ta dace, tare da sanar dasu cewa jami’an hukumar zasu biyo sawu domin tabbatar da cewa matasan basu sayar da kayan ba. Ya yi barazanar mika duk wanda aka kama da sauya akalar kayan zuwa hukumar EEFC.

Wakilinmu ya zanta da wasu daga cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin, daga karamar hukumar Yunusari, Fusama Alhaji Bai inda ya bayyana cewa, sun yaba matuka dangane da wannan tallafin da suka samu na gwamnatin Tarayya ta hanyar Sanata Gaidam.

Ya ce, “A matsayinmu na al’ummar mazabar Zone A suna alfahari da irin yadda Sanata Gaidam yake kokari wajen jawo hankalin gwamnatin tarayya domin inganta rayuwar yankunan da ke kan iyakar Nijeriya da makobciyarta Nijar. Wanda ko shakka babu hakan zai taimaka wajen farfado da yankunan.” In ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

Neymar Ya Zura Kwallaye 200 A Kungiyoyi Uku

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version