Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Sarkin Afaka Ya Jagoranci Tattaunawa Kan Zaman Lafiya

by Tayo Adelaja
September 18, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ibrahim Ibrahim, Kaduna

Masarautar Gundumar Afaka dake  Karamar Hukumar Igabi ta Jihar Kaduna, karkashin jagorancin Sarki Sani Musa Umar da hadin gwiwar hadakan kungiyoyin kabilun garin Afaka, sun jagoranci addu’oin zaman lafiya a gundumar na Garin Afaka,  da kuma kara tabbatarwa  Inyamurai cewa su cigaba da harkokin su kamar yadda suka saba.

samndaads

Taron addu’o’in ya samo asali ne sanadiyar zaman dar-dar da Inyamurai da wasu kabilu dake  zaune a gundumar suke  yi tun bayan da ‘yan ta’addan yankin Inyamurai suka lashi takobin ta’addanci a Kasa.

A Jawabinsa, mai girma Sarkin  Afaka Alhaji Sani Musa Umar, ya bayyana cewa,   “Zaman lafiya shi ne ginshikin rayuwa, idan babu zaman lafiya babu cigaba ga al’umma. Kuma Inyamuran Afaka muna zaman Lafiya da su saboda haka babu wani abin da zai raba kawunanmu.”

Sarkin  ya kara da cewa duk wani motsin da ba a gane ba,  ko kuma alamun wani na shirin tayar da zaune tsaye to ayi gaggawar sanar da hukuma, ko kuma a sanar da shi.

Daga karshe Sarkin  ya yaba wa gwamnatin tarrayya da ta Jiha, sannan kuma ya kara yabawa al’umman yankin Arewacin Kasar nan  dangane  da matakin da suka dauka domin hana daukar ramuwar gayya.

Kabilu da kungiyoyi daban-daban sun samu halartar taron, kuma kowanne wakili na kabila ko kungiyoyi sun tofa albarkacin bakinsu, inda kowa ya goyi bayan zaman lafiya.

A karshe an dauki lokaci mai tsawo ana addu’o’in neman zaman lafiya, wanda malaman addinin Kirista da na Musulmi suka jagoranta, Sannan mai girma  Sarkin Afaka  ya umurci Fastoci da Limamai su ci gaba da yin addu’o’i a Coci da Masallatai domin samun zaman lafiya mai dorewa na har abada.

SendShareTweetShare
Previous Post

Inyamurai Mazauna Bauchi Sun Barranta Kansu Da Biyafara

Next Post

Gwamnatin Nasarawa Ta Shiryawa Marasa Lafiya Tallafin Gaggawa

RelatedPosts

‘Yan Nijeriya Mutum Miliyan 15 Na Shan Kwayoyi, Inji Buba Marwa

‘Yan Nijeriya Mutum Miliyan 15 Na Shan Kwayoyi, Inji Buba Marwa

by Muhammad
32 mins ago
0

Shugaban Hukumar NDLEA mai yaki da sha da fataucin miyagun...

Katin Zama Dan Kasa

Nijeriya Ta Wajabta Wa Jami’an Diflomasiyya Mallakar NIN

by Sulaiman Ibrahim
7 hours ago
0

A jiya Lahadi Gwamnatin Tarayya ta shaida cewar, ya zama...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Kanawa Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Game Da Zaben Kananan Hukumomin Kano 

by Sulaiman Ibrahim
7 hours ago
0

A ranar Asabar din da ta gabata, 16 ga Janairu,...

Next Post

Gwamnatin Nasarawa Ta Shiryawa Marasa Lafiya Tallafin Gaggawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version