Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Sarkin Dokin Kara Bana Ya Gamu Da Fushin Hukuma A Kano

by Tayo Adelaja
September 20, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Na’ima Abubakar, Kano

Kamar yadda ya zama al’ada a duk shekara, matasa kan shirya wani kwarya-kwaryar Hawa amma na dokin Kara, Matasa a unguwar Fagge na cikin sahun matasan da kan yi irin wannan hawa a duk bayan sallah, idan Mai martaba Sarkin Kano ya kammala hawan Sallah. Su kuma irin wadannan matasa kan shirya nasu hawan domin nishadantar da al’ummar unguwannin su.

Wannan shekara Sarkin Dokin karan da aka fi sani da Sarki Jamilu ya fuskanci fushin hukuma alokacin da suka kammala shirin fita wannan hawa.

Kamar yadda aka saba ana taruwa a Masallacin waje inda anan ne sarkin ke karbar gaisuwar hakimansa, daga nan kuma sai a zagaya cikin unguwar Fagge inda ake gaisawa da jama’a, kuma Sarkin na tsayawa a wurare daban-daban idan jama’a ke yin gaisuwa harma ana yin addu’a. A ranar Asabar data gabata Sarki Jamilu da tawagar hakimansa suka  isa harabar Masallachin na Waje, daga nan ne kuma  sai jami’an tsaro suka zo  suka umarci sarki da ya kwance rawaninsa, Shi kuma Sarki Jamilu ya basu amsa da cewar Sarki baya kwance rawaninsa a titi, sai dai sarkin ya yiwa Jami’an tsaron alkawarin cewa daga na gida suka nufa.

Sarki Jamilu ya ci gaba da cewa daga nan ne kuma sai jami’an tsaron suka fara harbi sama, jama’a suka fara tsere, nima a raina har na yanke shawara guduwa sai na tuna sarki baya guda, guda sai kare sai doki, saboda haka nan na tsaya suka zo da mota suka ce ranka ya dade shiga na ce masu to na shiga matar tasu, domin ba gudu ba ja da baya, gara a matsayina na shugaba na tsaya duk abinda  zai sa me ni ya sa me ni maimakon jama’ata domin duk wanda ya zo wurin nan don mu yazo. Haka dai sarki Jamilu ya kwashe kwana guda a hannun jami’an tsaro sanann aka sako shi.

Tun kafi faruwa wannan al’amari rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta bayar da sanarwa hana duk wani taron al’umma wanda bata tabbatar da sahihancinsa ba domin kaucewa tashin tashina, kamar yadda kakakin rundunanr ‘yan Sandan Jihar Kano DSP Magaji Musa  Majiyar ya ambata.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Taimakon Al’umma Shi Ne Babban Burina –Hambali Shiitu

Next Post

Cibiyar Medicaid Za Ta Gudanar Da Taronta Na Shekara

RelatedPosts

Gwamnonin

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Bukaci Ma’aikatan Kotu Su Janye Yajin Aiki

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Kungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) da Taron...

Rasuwar

Al’umma Sun Kadu Da Rasuwar Madawakin Tsiga Magajin Amfani

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Abdullahi Sheme, A ranar Larabar da ta gabata ne...

Fityanul

Yadda Munazzamatul Fityanul Islam Ta Bude Sabon Reshenta A Garin Nyanya Da Ke Abuja

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, A ranar Lahadin da ta gabata,...

Next Post

Cibiyar Medicaid Za Ta Gudanar Da Taronta Na Shekara

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version