Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Sarkin Dokin Kara Bana Ya Gamu Da Fushin Hukuma A Kano

by Tayo Adelaja
September 20, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Na’ima Abubakar, Kano

Kamar yadda ya zama al’ada a duk shekara, matasa kan shirya wani kwarya-kwaryar Hawa amma na dokin Kara, Matasa a unguwar Fagge na cikin sahun matasan da kan yi irin wannan hawa a duk bayan sallah, idan Mai martaba Sarkin Kano ya kammala hawan Sallah. Su kuma irin wadannan matasa kan shirya nasu hawan domin nishadantar da al’ummar unguwannin su.

samndaads

Wannan shekara Sarkin Dokin karan da aka fi sani da Sarki Jamilu ya fuskanci fushin hukuma alokacin da suka kammala shirin fita wannan hawa.

Kamar yadda aka saba ana taruwa a Masallacin waje inda anan ne sarkin ke karbar gaisuwar hakimansa, daga nan kuma sai a zagaya cikin unguwar Fagge inda ake gaisawa da jama’a, kuma Sarkin na tsayawa a wurare daban-daban idan jama’a ke yin gaisuwa harma ana yin addu’a. A ranar Asabar data gabata Sarki Jamilu da tawagar hakimansa suka  isa harabar Masallachin na Waje, daga nan ne kuma  sai jami’an tsaro suka zo  suka umarci sarki da ya kwance rawaninsa, Shi kuma Sarki Jamilu ya basu amsa da cewar Sarki baya kwance rawaninsa a titi, sai dai sarkin ya yiwa Jami’an tsaron alkawarin cewa daga na gida suka nufa.

Tun kafi faruwa wannan al’amari rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta bayar da sanarwa hana duk wani taron al’umma wanda bata tabbatar da sahihancinsa ba domin kaucewa tashin tashina, kamar yadda kakakin rundunanr ‘yan Sandan Jihar Kano DSP Magaji Musa  Majiyar ya ambata.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Taimakon Al’umma Shi Ne Babban Burina –Hambali Shiitu

Next Post

Cibiyar Medicaid Za Ta Gudanar Da Taronta Na Shekara

RelatedPosts

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Harkokin Noma

Sarkin Noma Ya Shawarci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Kokari Wajen Gyara Harkokin Noma

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Bala Kukkuru, Sarkin Noman Jihar Kano, Alhaji Yusuf Umar...

Kwazon Tambuwal

Hobbasar Kwazon Tambuwal Na Fara Biyan Albashi Daga Haraji A 2023

by Muhammad
2 days ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Gwamnatin Jihar Sakkwato a karkashin jagorancin...

Next Post

Cibiyar Medicaid Za Ta Gudanar Da Taronta Na Shekara

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version