Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Kano Sanusi Da Ooni Na Ife Za Su Shiga Tsakani A Rikicin Gwamnati Da ASUU

by
3 years ago
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Kungiyar dalibai ta kasar nan tana ci gaba da kafa kwamitin shugabannin gargajiya da dattawar na kasar nan, domin su taimaka wajen kawo karshen rikicin gwamnati tarayya da kungiyar malaman jami’o’i na kasa wato ASUU da kuma kungiyar malaman kwaleji. A cewar shugaban kungiyar NANS, Danielson Akpan, wadanda za su jagoranci kwamitin dai su ne, Ooni na Ife, Oba Adeyeye Ogunwusi da kuma sarkin Kano Muhammadu Sanusi.
A cikin bayanin na ranar Lahadi, kungiyar daliban ta bayyana cewa, a cikin kwamitin shugabannin gargajiyar wanda za su shiga takanin gwamnatin tarayya da kuma kungiyar ASUU sun hada har da sarkin Onitsha, Nnaemeka Achebe da kuma Olawo na Owo, Dakta Bictor Olateru-Olagbegi.
Shugaban dattawan kwamitin sun hada da Cif Edwin Clark, Alhaji Tanko Yakassai, Aare Afe Babalola, Cif Innocent Chukwuma, Misis Folorunso Alakija, Farfesa Suleiman Bala Mohammed da kuma shugaban jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi, Farfesa Rukayat Mohammed tsohuwar minister ilimi.
Mashahuran Lauyoyi guda biyu Messrs Femi Falana da kuma Kayode Ajulo, su ma suna cikin kwamitin.
Akpan ya bayyana cewa, kwamitin zai tattauna da kungiyar ASUU da ASUP da kungiyar ma’ikatan ilimi da masu ruwa da tsaki da kuma gwamnatin tarayya, domin su kawo karshen rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa a harkar ilimin kasar nan.
Ya ce, “Tarihi ya nuna cewa ilimi yana da inganci a Nijeriya kamar yadda yake a sauran kasashen duniya, inda wasu ‘yan kasashe suke zuwa jami’o’in Nijeriya. Kafin shekarar 1988 lokacin da aka kafa kungiyar malaman jami’o’in wanda ake kira a yanzu da suna yajin aikin ASUU.
“Ba saban abuba ne a Nijeriya cewa yajin aikin kungiyar ASUU ya kawo wa harkar ilimi cikas a wannan kasa, haka kuma sauran kungiyoyin ilimi suna sun bi sawu. Saboda haka, mun fara tattaunawa tare da samun goyan bayan dattawa da shuwagabannin al’umma ta yadda za a ta zauna da kungiyar ASUU, ASUP,COEASU da sauran kungiyoyi da masu ruwa da tsaki tare da gwamnatin tarayya ta yadda za a kawo karshan lamarin yajin aiki a Nijeriya.”

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Jami’an SARS Sun Kashe Matashi A Wurin Kallon Kwallo A Legas

Next Post

An Sako Ma’aikacin Gwamnatin Taraba Bayan Biyan Naira Miliyan 5

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
32 mins ago
0

...

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan  Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

by Sulaiman Idris
2 hours ago
0

...

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

Kisa Kan Zargin Batanci Ga Annabi: An Tsare Wadanda Aka Kama A Gidan Gyara Hali

by
3 hours ago
0

...

An Yi Lugudan Wuta Ta Jiragen Yaki Kan Isis An Kashe Kwamandanta Bin-umar A Tabkin Chadi

Dakarun MNJTF Sun Yi Barin Wuta Kan ‘Yan Boko Haram Sun Kashe 300 A Tafkin Chadi

by Leadership Hausa
4 hours ago
0

...

Next Post
Garkuwa

An Sako Ma’aikacin Gwamnatin Taraba Bayan Biyan Naira Miliyan 5

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: