Ahmed Muhammad Dan Asabe">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Sarkin Koton Karfe Ya Kaddamar Da Ajujuwan Da Shirin SDG Ya Gina

by Ahmed Muhammad Dan Asabe
December 7, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Sarkin Koton Karfe Ya Kaddamar Da Ajujuwan Da Shirin SDG Ya Gina
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Mai martaba Sarkin Koton karfe (Ohimege Igu), Alhaji Abdulrazak Gambo Isah Koto, ya kaddamar da ajujuwan karatu shida a makarantar yaran yan sanda da kuma wasu ajujuwan shida a makarantar sakandiren yan mata da ke garin Koton karfe a jihar Kogi, ranan asabar daya gabata.

Ofishin babban mai bai wa shugaban kasa shawara akan shirin raya muradi mai dorewa (SDG) ne, ya bada kwangilar ayyukan,amma kuma Alhaji Hassan Shu’aibu Ohimozi ne yayi sanadiyar bayar da kwangilar ayyukan a makarantun biyu.
Sarkin na Koton karfe ya yabawa Alhaji Hassan shu’aibu Ohimozi a bisa yin amfani da damar da ya samu na kawo ci gaba a yankin.
Ya kuma yi amfani da bikin wajen kira ga yan asalin yankin mazansu da matansu masu hannu da shuni da suyi koyi da Alhaji Hassan Ohimozi, sannan ya yaba masa a bisa kaunar yankin.
Alhaji Abdulrazak Isah Koto ya kuma nanata bukatar zaman lafiya a yankin,inda yace ko kadan babu yadda za a samu ci gaba mai ma’ana sai da zaman lafiya mai dorewa, sannan ya bukaci jama’ar masarautarsa dasu ci gaba da zaman Lafiya da junansu don amfanin yankin.
Da ya ke jawabi a wajen bikin, Alhaji Hassan Shu’aubu Ohimozi,wanda shine salsalar samar da ayyukan biyu, yace a matsayinsa na malamin makaranta, yayi farin ciki matuka gaya ganin cewa shirin na SDG ya wanzar da ayyukan a yankin daya fito.
Daga nan ya yabawa ofishin shirin SDG a bisa samar da ayyukan, sannan yace zai ci gaba da yin bakin kokarinsa wajen ganin ya kawo ayyukan ci gaba zuwa al’ummarsa, inda ya kara da cewa nan da yan kwanaki masu zuwa za a samar da cibiyar kiwon lafiya a kauyen Edagaki da ke yankin na Koton karfe.
Shi ma a nasa jawabin, Alhaji Usman Audu Shu’aibu wanda ya wakilci babban mai bai wa shugaban kasa shawara akan shirin SDG,yace Alhaji Hassan Ohimozi ne kashin bayan gina ajujuwan, kana ya jinjina masa a bisa kishin al’ummarsa.
Haka shi ma da ya ke jawabi, mai bai wa gwamna Yahaya Bello shawara akan shirin SDG, Alhaji Nasiru Isah Ohiani yace ayyukan sun zo dai dai akan lokacin da a ke bukatansu, sannan ya bukaci al’ummar yankin da su kare da kuma kula da ayyukan biyu.
A jawabansu dabam dabam, shugaban makarantar yaran yan sanda da na makarantar sakandiren yan mata wadanda makarantunsu ne su ka ci gajiyar shirin na SDG, duk sun jinjinawa kokarin Alhaji Hassan Shu’aibu Ohimozi a bisa yin amfani da damarsa wajen janyo ayyukan zuwa makarantunsu.
A kan haka nema su ka yi kira ga yan asalin karamar hukumar ta Koton karfe wajen ganin sun yi koyi da Alhaji Hassan Shu’aibu Ohimozi wanda a cewarsu mutum ne wanda keda kishin yankin daya fito.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

A Daina Kyamatar Wadanda Suka Fito Daga Gidajen Yari – Kwanturola Labbo

Next Post

Rikon Jam’iyya Ba Na Gwamna Ba Ne, In Ji Danjuma Bakin Wafa

RelatedPosts

Ebonyi

Kwamishinan ’Yan Sandan Ebonyi Ya Kama Hadiman Gwamnan Jihar Biyu Da Shugaban Karamar Hukuma

by Ahmed Muhammad Dan Asabe
17 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Rundunar 'yan sanda ta kama wasu...

Direbobi

Bakwai Sun Mutu Da Yawa Sun Jikkata A Rikicin Shugabancin Kungiyar Direbobi

by Ahmed Muhammad Dan Asabe
17 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, A kalla mutane bakwai ne suka...

Takalmi

Mata Ta Rafka Wa Mijinta Tsinin Dunduniyar Takalmi Ya Mutu

by Ahmed Muhammad Dan Asabe
17 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Wata mata da ba a bayyana...

Next Post
Rikon Jam’iyya Ba Na Gwamna Ba Ne, In Ji Danjuma Bakin Wafa

Rikon Jam’iyya Ba Na Gwamna Ba Ne, In Ji Danjuma Bakin Wafa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version