Sarkin Musulmi Ga Malamai: Ku Rika Shawartar Masu Mulki Kan Shugabanci Nagari
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Musulmi Ga Malamai: Ku Rika Shawartar Masu Mulki Kan Shugabanci Nagari

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Sarkin Musulmi

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Abubakar ya bukaci malamai da su rika shawartar masu mulki kan shugabanci nagari.

Sarkin Musulmin ya yi wannan kiran ne a Abuja wajen taron bitar ga malaman addini kan harkokin kiwon lafiya a matakin farko.

  • Ranar Litinin Za A Kaddamar Da Jirgin Kasan Legas Da Zai Rika Jigilar Fasinja 175,000
  • NIS Ta Bude Ofishin Samar Da Ingantaccen Fasfo A Zariya

Kamfanin dillancin labara na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa ma’aikatar lafiya da jin dadin jama’a ta tarayya tare da hadin gwiwar hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa (NPHCDA) ne suka shirya taron.

Sarkin Musulmi ya ce yana da kyau malamai su kasance masu gaskiya da rikon amana a yayin da suke da kusanci da shugabannin siyasa.

“Shugabannin addini sukan rike mukamai masu gwabi kuma suna iya kawo sauyi ga rayuwar al’umma.

“Ta hanyar ba da shawara ta gaskiya ne za a iya samun ingantacciyar shugabanci da zai ba da gudummawa ga rayuwar al’ummarsu gaba daya.

“Kyakkyawan sadarwa tsakanin malamai da shugabannin siyasa na iya haifar da fahimtar juna, hadin kai da kuma cimma manufofin da aka saka a gaba.

“A duk lokacin da malamai ke fada wa masu mulki gaskiya, zai taimaka wajen yanke hukunci da manufofi wadanda suka dogara a kan ingantattun bayanai da suka dace da dabi’u da ka’idodi,” in ji shi.

Shi ma shugaban kungiyar Kiristocin Nijeriya (CAN) Archbishop Daniel Okoh, ya bukaci karin hadin kai da hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa domin inganta harkokin kiwon lafiya musamman a yankunan karkara.

 Okoh, wanda ya bayyana muhimmiyar rawar da malaman addini suke takawa wajen bayar da shawarwari da wayar da kan jama’a, ya ce dole ne a hada kai da shugabannin siyasa domin inganta harkar kiwon lafiyar kasar nan.

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate, ya yaba wa gudunmawar da malamai ke bayarwa wajen samar da kiwon lafiya a kasar nan.

Ministan ya jaddada mahimmancin hadin gwiwa tsakanin gwamnati da malaman addini.

Pate ya ja hankali kan yadda fannin kiwon lafiya ke ci gaba da bunkasa, ya ce akwai bukatar yin hadin gwiwa a tsakanin ma’aikatan kiwon lafiya da malamai.

“Ta hanyar hadin kai ne za a samu damar ilimantar da juna da kuma sanar da jama’a game da abubuwan da ke faruwa, za mu tabbatar da cewa an samar da ayyuka masu inganci na kiwon lafiya ga ‘yan Nijeriya,” in ji shi.

Babban daraktan hukumar NPHCDA, Dakta Faisal Shuaib, ya yi kira ga malamai da su ba da himma gudunmuwa wajen inganta harkokin kiwon lafiya a matakin farko da kyautata jin dadin al’umma.

“Manufar wannan taro na musamman shi ne, rigakafin cutar kansa ta mahaifa ta hanyar allurer HPB,” in ji shi.

Ya bukaci shugabannin addini da su bayar da shawarwarin rigakafi a cibiyoyinsu.

Shugaban NPHCDA ya jaddada karfin hadin kai da aiki tare wajen inganta lafiya da walwalan al’umma.

Ya ce ta hanyar hada kai ne malamai da ma’aikatan kiwon lafiya za su bayar da gudummuwa ga harkokin lafiya da kuma ci gaban kasa.

NAN ta ruwaito cewa taron ya samu halartar malaman addini, ma’aikatan lafiya da masu ruwa da tsaki kan harkokin lafiya da manyan jami’an gudanarwa na ma’aikatar lafiya da NPHCDA.

Taron dai an yi shi ne domin kara inganta fahimtar malamai game da allurar rigakafi da sauran shirye-shiryen kiwon lafiya tare da wayar da kan al’umma kan amfanin rigakafin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Japan

Amurka Tana Goyon Bayan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Yayin Da Ta Rage Shigo Da Kaya Daga Japan

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version