Saurayi Ya Kashe Budurwarsa A Kan 5000 A Bauchi
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saurayi Ya Kashe Budurwarsa A Kan 5000 A Bauchi

bySadiq
2 years ago
Saurayi

Wani matashi mai shekaru 19 mai suna Mohammed Ibrahim, mazaunin Sabon-Layi da ke wajen birnin Bauchi a Jihar Bauchi, ya daba wa budurwarsa mai suna Emmanuella Ande wuka har lahira bayan wani rikici da ya barke a tsakaninsu kan kudi naira 5,000.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa kafin faruwar lamarin, Mohammed ya sace kusan Naira 400,000 na mahaifinsa domin ya kashe wa Emannuella, wadda ‘yar Jihar Filato ce, bayan sun shirya haduwa a Fatakwal a Jihar Ribas.

  • Mahara Sun Sace Sarki Da Fadawansa A Garin Pupule Na Jihar Taraba
  • Gwamnati Ta Shirya Fatattakar ‘Yan Bindiga A Duk Inda Suke – Ministan Tsaro

Mohammed wanda yanzu haka yana hannun ‘yansanda, ya hadu da marigayiyar ne a shafukan sada zumunta kafin daga bisani suka hadu a wani wurin shakatawa da ke unguwar Bayan-Gari a Bauchi.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, SP Ahmed Mohammed Wakil, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Laraba, ya ce wanda ake tuhumar ya kuma daba wa wani Zaharadeen Adamu mai shekaru 36 wuka, wanda ya yi kokarin ceton Emmanuella.

“Wannan mummunan al’amari ya faru ne a lokacin da wadda aka kashe ta bukaci kudi naira 5000 yayin da ita budurwar ta nemi ya biya ta wasu da ta ke bin sa, hakan ne ya sa cacar-baki ta kaure har fads ya shiga tsakaninsu lamarin da ya yi sanadin da ya sa ta samu rauni wanda ya kai ga mutuwarta.

“Ya daba wa budurwarsa Emmanuella Ande ‘yar Jihar Filato, wuka a kusa da kirjinta, a lokacin ne budurwar ta yi kururuwa, mutanen da ke wajen suka yi yunkurin kai mata dauki, suka bude kofar da karfi, inda wanda ake zargin ya kuma daba wa daya daga cikinsu wuka.

“Tawagar ‘yansanda ta yi gaggawar kai dauki, inda suka dauki budurwar zuwa asibitin koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH) Bauchi, inda aka tabbatar da mutuwarta.

“Haka zalika, an kwantar da Zaharadeen kuma an yi masa magani a asibitin an kuma sallame shi, a halin yanzu ana bincike a kan lamarin,” in ji kakakin.

SP Wakil ya ce an samu wuka daga hannun Mohammed, inda ya kara da cewa ana ci gaba da gudanar kammala bincike, za a gurfanar da wanda ake zargin a kotu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

Sin Ta Kara Tallafin Kudi Don Maido Da Wuraren Kiyaye Ruwa A Yankunan Da Girgizar Kasar Ta Shafa

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version