Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Sauya Fasalin Nijeriya: Dole Arewa Ta yi Magana Da Murya Daya -Gwamna Masari

by Tayo Adelaja
September 26, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga El-Zaharadeen Umar, Katsina

Gwamna Aminu Bello Masari  na Jihar Katsina ya bayyana cewa akan batun sake fasalin Najeriya dole ne arewa ta yi magana da murya daya domin kare muradun mutanan da ake wakilita.

samndaads

Alhaji Aminu Bello Masari ya fadi haka ne a lokacin taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar APC ta gudanar a gidan gwamnatn jihar Katsina, domin kowa ya bada tasa gudunmawa da za a tunkari wannan taro na jin ra’ayoyin jama’a akan gyara fasalin kudin tsarin mulkin Kasar nan.

Haka kuma gwaman ya ce wannan ba wai batu bane da mutun daya ba, abu ne da ya shafi al’umma, saboda haka ya zama wajibi kowa ya bada tasa gudunmuwa, indai dan asaliin Katsina ne, ba tare da nuna banbancin siyasa ba, magana ake ta kasa baki daya.

Haka kuma gwamnatin jihar Katsina ta kafa wani kwamitin da zai tuntubi wadanda suke da ruwa da tsaki a karkashin jagorancin tsohon gwamnan jihar Katsina, Alhaji Sa’idu Barda da wasu manyan mutane na wannan jiha, domin su ka wo mutane da za su shi ga cikin wannan lamari.

Ya kara da cewa idan ana maganar tsarin mulki to ana maganar abin da ya shafi rayuwar mutane, dole akwai malaman addini, domin ya zuwa yanzu an fara samun ra’ayoyi ma bambanta da suka shafi addini inda wasu ke ganin ya kamata a canza tsarin mulkin a koma na asali.

Tun da farko a jawabinsa na maraba shugaban jam’iyyar APC a jihar katsina Malam Shitu S. Shitu ya bayyana cewa dalilin wannan taro shi ne domin a tattauna akan wannan mahimmin batu na gyara fasali tsarin mulkin kasa, sannan daga baya za su shiga wani batu da ya shafi jam’iyyar APC a jihar Katsina.

Shugaban Jam’iyyar ya kara da cewa tun farkon wannan tafiya babu wani hakki da ya shafi jam’iyya wanda gwamnatin jihar Katsina bata sauke ba, saboda haka yana ganin abin da kawai ya fi shi ne, su kara dinke barakar da ke tasowa.

Malam Shitu. S. Shitu ya shawarci mutanan Katsina da su tabbatar sun bada ta so gudunmawa wajan wannan batu mai matukar mahimmin, da ya shafi rayuwar mutanan arewa da Najeriya baki daya domin gudun kadda a bar arewa a baya.

Daga karshe an bada dama ga mahalarta taron su bayyana abin da suke ganin ya kamata ayin akan batun da ya shafi sauya fasalin Kasa da ake tunkara a halin yanzu.

Haka kuma taron ya samun halarta shugabanin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki na jihar Katsina da ‘yan majalisar tarayya da na jaha da ‘yan kasuwa da kuma ‘yan kwangila, daga bisani kuma a rufe kofa domin ci gaba da tattaunawa akan abin da ya shafi jam’iyyar a matakin jiha, inda manema kabarai suka fita daga dakin taron.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Tsige Mataimakin Kakakin Majalisar Adamawa

Next Post

Dausayin Musulunci Musulunci Daya Ne, Saboda Cikarsa Yana Da Matakai Uku (2)

RelatedPosts

Gwamnan Bauchi Ya Amince Da Murabus Din Sakatarenshi

Gwamnan Bauchi Ya Amince Da Murabus Din Sakatarenshi

by Muhammad
3 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad...

Fitaccen Dan Jarida A Duniya, Larry King, Ya Rasu

Fitaccen Dan Jarida A Duniya, Larry King, Ya Rasu

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Fitaccen mai watsa shirye-shiryen talabijin da rediyo, Larry King, wanda...

EFCC Ta Cafke ‘Yan Damfarar Intanet 11 A Osogbo

EFCC Ta Cafke ‘Yan Damfarar Intanet 11 A Osogbo

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

EFCC ta cafke wasu mutane 11 da ake zargi da...

Next Post

Dausayin Musulunci Musulunci Daya Ne, Saboda Cikarsa Yana Da Matakai Uku (2)

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version