Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

byLeadership Hausa
2 months ago
APC

A yanza haka sanatoci biyu kacal ya rage wa jamƴyar APC ta samu kashi biyu cikin uku na yawan ƴan majalisar dattawa, sakamakon sauya sheƙa da sanatoci guda huɗu suka yi daga PɗP zuwa APC a ranar Laraba da ta gabata.

Bisa tsarin kundin mulkin Nijeriya da dokokin majalisar ƙasa, wannan na nufin cewa idan APC ta samu kashi biyu bisa uku na yawan mambobi a majalisar dattawa, kowanne ƙudirin doka ko wata buƙata da aka kawo zauren majalisar dattawa dole sai ya samu goyon bayan APC kafin a amince da shi ko ba tare da goyon bayan ƴan adawar ba. 

Masana sharhi kan harkokin siyasa su yi gargaɗin cewa irin wannan rinjaye na haifar da babbar barazana ga dimokuraɗiyyar Nijeriya da ke tasowa kuma yana iya haifar da mulkin kama-karya.

  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Sake Ciyo Bashin Dala Biliyan 21 Daga Ƙetare
  • Wasu Gwamnonin PDP Sun Kulla Makirci Kan Samun Shugaban Kasa Daga Yankin Kudu —Wike

Sanatocin guda hudu da suka sauya sheƙa a makon da ya gabata sun kasance biyu daga Jihar Akwa Ibom da kuma daga Jihar Osun, sun bayyana ficewarsu a lokacin taron zaman majalisar. Sanatocin sun hada da Sanata Sampson Ekong, mai wakiltar Akwa Ibom ta kudu da Aniekan Bassey, mai wakiltar Akwa Ibom ta arewa maso gabas da Francis Fadahunsi, mai wakiltar Osun ta gabas da kuma Olubiyi Fadeyi, mai wakiltar Osun ta tsakiya.

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya karanta wasiƙar sauya sheƙar a zauren majalisar.

Saboda haka, ƙarfin APC a zauren majalisar dattawa mai mambobi 109 ya kai 70, kujeru biyu kadai take buƙata ta cika 72 don samun rinjaye na kashi biyu cikin uku.

PɗP yanzu haka tana da kujeru 28, yayin da jam’iyyar LP ke da biyar. Jam’iyyar SɗP na da kujeru biyu, yayin da jam’iyyar NNPP da APGA ke da kujeru guda daya kowannansu.

A yanzu haka, akwai kujeru biyu na majalisar dattawa da babu kowa. Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), har yanzu ba ta gudanar da zaɓen cire gurbin Sanata Ifeanyi Ubah, mai wakiltar Anambra ta kudu, wanda ya rasu a farkon wannan shekara, da Sanata Monday Okpebholo, mai wakiltar Edo ta tsakiyar, wanda ya bar kujerarsa bayan lashe zaɓen gwamna na Jihar Edo a 2024.

Kazalika, a majalisar wakilai ma an samu sauya sheƙar mambobi guda uku daga PɗP zuwa APC a ranar Laraba, wanda ya kuma ƙara ƙarfafa ƙarfin jam’iya mai mulki zuwa samun kujeru 224 a cikin kujeru 360 na majalisar. ƴan majalisar wakilan da suka saura sheƙa sun hada da Taofeek Ajilesoro da Omirin Emmanuel Olusanya daga Jihar Osun, tare da Marcus Onobun daga Jihar Edo da kuma Mark Esset daga Akwa Ibom.

Bisa wannan lamari, PɗP yanzu tana da kujeru 86, yayin da jam’iyyar LP take da kujeru 26, NNPP ta da 16, APGA ta da shida, SɗP ta da biyu, sannan ADC tana da daya.

A halin yanzu, akwai kujeru biyar a majalisar wakilai da babu kowa sakamakon mutuwar ƴan majalisar guda huɗu da kuma daya da ya yi murabus.

da yake tsokaci kan samun rinjayen APC a zauren a majalisun tarayya a gaban zabɓen 2027, masana kimiyyar siyasa, Farfesa Gbade Ojo, ya yi gargaɗi game da mummunan sakamako ga makomar dimokuraɗiyyar Nijeriya.

Ya ce, “Abin da muke shaida shi ne, APC na ƙara samun gagarumin rinjaye. ɗuk da cewa hakan na iya bayyana matsayin siyasa mai ƙarfi a zahiri, tasirin wannan ga dimokuraɗiyya yana da matukar damuwa. 

“Lokacin da wata jam’iyyar mai mulki a cikin dimokuraɗiyya ta mamaye majalisa har ta samu kashi biyu cikin uku na yawan mambobi, hakan yana zama wani siffofi na mulkin kama-kurya, domin ba za a samu ingantaccen kulawa da daidaito ba,” in ji shi.

Ya ba da shawara cewa a irin wannan yanayi, majalisun tarayya na iya rasa ƴancin kai da zama ƴan amshin shata ga ɓangaren zantarwa.

Ya gargaɗin cewa in har ƴan adwa ba su sake tsarawa ba ta hanyar dawo da tsaftataccen tsarin cikin gida da kafa wani takamaiman aƙidar tunani, dimokuraɗiyyar Nijeriya za ta ci gaba da kasancewa cikin hatsari da rashin daidaito.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version