Sulaiman Ibrahim">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

by Sulaiman Ibrahim
January 22, 2021
in LABARAI
2 min read
Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, ayau Juma’a, ta ce shirin Gwamnatin Tarayya na shirin sayar da kadarorinta zai amfani ’yan Niieriya kuma zai taimaka wajen bunkasa tattalin arziki.

Ta bayyana hakan ne a yayin zantawarta da gidan talabijin na Channels a shirin Sunrise Daily, Ahmed, wacce kuma ita ce Ministar Kasafin Kudi da Tsare-Tsare ta Kasa, ta ce a yanzu haka wasu kadarorin gwamnati sun mutu kuma basu da kima ko daraja ko kadan ga ’yan Nijeriya a halin da suke ciki.

samndaads

Ministan ta ce “Akwai wasu kadarorin gwamnati da suka mutu wadanda za a iya sayarwa kamfanoni masu zaman kansu don sake farfado da su don amfanin ‘yan Nijeriya.”

“Don haka muna duba daban-daban – kuma ni memba ce ta Majalisar Kula da sayar da kadarorin gwamnati – muna duba bangarori daban-daban na kadarorin gwamnati wadanda gwamnati ba ta iya sarrafawa, to ya dace a mika su ga kamfanoni masu zaman kansu.

A yau Juma’a, Ahmed ta jaddada cewa “niyyar ba wai kawai a samar da cikon kudin kasafin ba ne, akwai bukatar sake farfado da wadannan kadarorin tare da mika su ga kamfanoni masu zaman Kansu don bada gudummawa ga ci gaban tattalin arzikin Kasa.”

Ta kara da cewa Ofishin ma’aikatun gwamnati zai fara hada kai da sauran bangarorin gwamnati kan siyar da kadarorin a farkon zangon shekarar.

A cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, kungiya mai kula da dukiyoyin gwamnati mai zaman kanta SERAP ta nemi Majalisar Dokoki ta kasa da ta dakatar da gwamnatin tarayya daga sayar da kadarorin jama’a don daukar nauyin kasafin kudin 2021.

Kungiyar ta ce, a maimakon haka, ya kamata gwamnati ta sake duba wasu fannoni a cikin kasafin kudin don rage yawan kudin kasafin, kamar rage yawan albashi da alawus-alawus ga jami’an gwamnati.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kawuna Ya Turo Ni Kano Don Yin Garkuwa Da Mutane, In Ji Maryam  

Next Post

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

RelatedPosts

Sarkin Musulmi

Fulani Ba ‘Yan Ta’adda Ba Ne –Sarkin Musulmi

by Sulaiman Ibrahim
17 hours ago
0

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammadu Sa’ad Abubakar III, ya ce...

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

by Sulaiman Ibrahim
22 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Gusau A shirin Gwamnatin Jihar Zamfara na...

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

by Sulaiman Ibrahim
22 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Mohammed, Matawallen...

Next Post
Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version