Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Secondus Ya Aza Tubalin Ginin Hanyoyin Biliyan 12 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
December 17, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Secondus
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa, Prince Uche Secondus ya aza tubulin ginin wasu manyan hanyoyi guda biyu a karkashin shirin fafada fadar jihar Bauchi.

Har-ila-yau, shi ma gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal ya kaddamar da wasu ayyukan hanyoyin guda biyu dukka a cikin kwaryar garin Bauchi wanda gwamnatin jihar ta bada su.

samndaads

Hanyoyin sun hada da maida babban hanyar da ta taso daga titin Awala zuwa filin sauka da tashi na jiragen kasa da kasa da ke Bauchi tare da maida shi daga layi daya zuwa tagwayen hanyoyi; sai kuma maida hanyar da ya tashi daga Awalah zuwa jami’ar jihar Bauchi da ke kan titin zuwa Maiduguri zuwa tagwayen hanyoyi daga hanya mai layi daya; da kuma hanyar Dogon Yaro zuwa Zarandan Otel gami kuma da hanyar da ta tashi daga gidan man Mobile ya nausa zuwa mahadalar ofishin ‘yan kwana-kwana da ke jihar.

Dukkanin ayyukan sun kai kilomita 26 da aka bada kudinsu a kan kwangila naira biliyan 12. Wadannan ayyukan dai gwamnan jihar ta Bauchi Bala Muhammad ne zai gudanar da su a bisa muradinsa na sabuntawa da inganta jihar Bauchi.

Uche ya shaida cewar ba su yi mamakin namijin kokarin da gwamnan ke yi a Bauchi ba, muddin aka yi la’akari da irin himma da kwazon da ya nuna a lokacin da yake Ministan babban birnin tarayya Abuja, ya nuna kwarin guiwarsa na cewa tabbas al’ummar Bauchi za su mori gwamnatin Bala sosai.

Secondus ya tabbatar da cewar da zarar aka kammala wadannan ayyukan za su kai ga bunkasa tattalin arzikin jihar, inganta hanyoyin yawon bude ido da shakatawa musamman domin kara samar da maziyarta zuwa gandun dujin Yankari mai dumbin tarihi tare da wasu tulin alfanu da hanyoyin za su samar wa jihar.

Shi kuma a jawabinsa, gwamnan jihar Bala Muhammad, ya nuna cewa sun yi nazarin cewa jihar tana gayar bukatar muhimman ayyukan da za su fadadata tare da inganta jihar.

Ya shaida cewar nan da shekaru biyu ake son kammala wadannan ayyukan da aka kaddamar da su, baya ga wadannan, ya shaida cewar akwai muhimman ayyukan gina titina da gadaje da yanzu haka gwamnatinsa take kai da kuma wadanda ta samu nasarar kammalasu tun lokacin da ta zo kan mulki.

Ya kuma ce, za su cigaba da gudanar da ayyukan da za su kyautata jihar, inda ya gode wa majalisar dokokin jihar a bisa hadin kai da goyon bayan da suke ba shi a kowani lokaci wajen tabbatar da aiwatar da ayyukan da suka dace.

Shi ma da ya ke tofa albarkacin bakinsa, gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwal, ya misalta hanyoyin da aka kaddamar da fara yinsu a matsayin hanyoyi da za su kara wa jihar Bauchi tagomashin samun ababen more rayuwa da daman gaske, tare da bunkasa harkokin kasuwanci.

Ya ce, samar da hanyoyi masu nagarta na kara sada jama’a da jama’a wanda kuma ake riskar dumbin ababen more rayuwa matuka gaya.

SendShareTweetShare
Previous Post

2023: Tsoffin Sanatoci Da ’Yan Majalisa Sun Bukaci Tinubu Ya Tsaya Takara

Next Post

’Yan Kasuwar Arewa Mazauna Legas Sun Kaddamar Da Sabuwar Kungiya

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Khalid Idris Doya
12 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Khalid Idris Doya
12 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Khalid Idris Doya
12 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
’Yan Kasuwar Arewa

’Yan Kasuwar Arewa Mazauna Legas Sun Kaddamar Da Sabuwar Kungiya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version