Sha'aban Sharada Ya Maka Dan Takarar Gwamnan APC Na Kano A Kotu
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sha’aban Sharada Ya Maka Dan Takarar Gwamnan APC Na Kano A Kotu

bySadiq
3 years ago
Sha'aban

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Birni a Jihar Kano , Sha’aban Sharada, ya shigar da kara a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Kano, inda yake neman ta soke takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Nasiru Gawuna, a matsayin dan takarar gwamna a 2023 na jam’iyyar APC a jihar.

Dan majalisar wanda ke wakiltar mazabar karamar hukumar Birni, ya bukaci kotun da ta soke zaben saboda zargin aikata rashin adalci yayin gudanar da zaben fidda-gwanin.

  • Yadda Noman Rani Ya Rage Kwararowar Mutanen Kauye Zuwa Birni
  • Hadin Gwiwar BRICS Ya Kai Matsayin Koli

Duk da zabar Gawuna tare da tsohon kwamishinan kananan hukumomi Murtala Garo da wakilan jam’iyyar APC na Kano suka yi a matsayin ‘yan  takarar gwamna, Sharada bai gamsu da zaben ba.

Sha’aban na neman a soke zaben fidda gwanin da aka gudanar na zaben Gawuna a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar, inda ya ce an sabawa dokar zabe ta 2022.

A wata takardar karar da ya shigar gaban babbar kotun tarayya da ke Kano, wanda ya shigar da karar ta hannun lauyansa J. O. Asoluka, SAN, ya ce zabar Gawuna ya sabawa sashe na 84 (1),(3),(8),(12). da (13) na dokar zabe da aka yi wa kwaskwarima.

Bugu da kari, lauyan wanda ya shigar da karar, inda ya bayyana cewa saba tanadin dokar da kuma ka’idojin jam’iyyar APC, gwamnatin jihar ta yi magudin zaben wakilai tare da tilasta musu zaben wanda ba su da ra’ayin zaba.

Ya kuma nuna damuwarsa kan yadda zaben fidda gwanin ya gudana wanda ya bai wa masu rike da mukaman siyasa damar kada kuri’unsu duk da sashe na 84 (13) na dokar zabe wanda ya hana su shiga zaben fidda gwani.

A halin da ake ciki, mai shari’a Liman, ya bayar da izinin yin aiki da wasu kararraki biyu da mai shigar da kara ya gabatar.

Kotun ta dage sauraren karar daga kwanaki 30 zuwa kwanaki 15 domin a gaggauta sauraren shari’ar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa
Manyan Labarai

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025
Next Post
Ya Ake Ciki Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta 2022 A Qatar?

Ya Ake Ciki Game Da Gasar Cin Kofin Duniya Ta 2022 A Qatar?

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version