Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA TEBURIN EDITA

Sharar Fage Daga Alkalamin Edita

by Tayo Adelaja
September 17, 2017
in DAGA TEBURIN EDITA
4 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

08148507210 (TES Kawai )  leadershipayau.com       

Sallama cikin aminci a gare ku ya ku makaranta wannan jarida ta LEADERSHIP A YAU LAHADI. Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai. Tsira da amincin Allah Ya tabbata ga shugaban halitta, Muhammad Dan Abdullah.  Bayan haka, Ina mai gabatar mu ku da wannan jarida mai albarka a karon farko, sannan kuma Ina mai gabatar mu ku da wannan shafi mai taken MAHANGA, wanda zai cigaba da fitowa a bangon bayan jaridar nan taku mai albarka.

samndaads

To, amma ku sani cewa, a matsayina na edita ba ni ne zan rika yin rubutu a wannan shafi ba, har sai dai idan hakan ta kama. Daraktan Editoci da kansa, Malam Musa Muhammad, ne zai rika tattaunawa da ku a wannan shafi. A yau Ina yin sharar fage ne kawai; Ina share wa babban daraktanmu hanya.

LEADERSHIP A YAU LAHADI za ta kasance ta tsaya tsayin daka wajen tabbatar da kare muradun kasa, kwato wa wanda a ka tauye hakkinsa, jajircewa wajen tabbatar da gaskiya tare da fadakarwa da nishadantarwa.

Ba wai kawai matsalar za mu tattaunawa a kai ba, illa dai za mu yi kokari mu ga cewa, mun zo wa da dukkan masu ruwa da tsaki, kan duk batun da mu ka dauko, cikakkiyar mafita, domin a taru a fitar da jaki daga cikin duma.

Hakika Nijeriya ta na fama da matsaloli daban-daban, wadanda su ka hada da matsalar tattalin arziki, matsalar tsaro, matsalar ’yan bil adama, matsalar cin hanci da rashawa, matsalar kabilanci, matsalar bangaranci, rikice-rikicen addini, nakasun siyasa da dimukradiyya ita kanda da dai sauran matsaloli da su ka dabaibaye kasar kuma su ke kawo ma ta dabaibayi da tarnaki wajen cigabanta.

Bias la’akari da arzikin da Nijeriya ke da ita, yakamata a ce kawo yanzu irin wadannan matsaloli da mu ka zayyana a sama, an wuce a kasar ta yadda bai kamata a ce har yanzu su ne manyan matsalolinmu ba. Ya fi dacewa a ce, yanzu matsalarmu ita ce ta yadda za mu iya kera abubuwan da wasu kasashen duniya ba su kera sub a.

Wato ya zamana cewa, kamata ya yi na ce gasar cigaban duniya mu ke yi ta hanyar jera wa kafada da kafada da sauran manyan kas ashen duniy. Amma babban abin takaici ne a ce har yanzu mu na maganar ginin hanyoyi, ajijuwa, albashi, ruwan sha, wutar lantarki, magani a aisibiti da sauran abubuwan da tuni duniya ta mance da matsalarsu! Babban abin kunya ne a ce har yanzu akwai kasuwar janareto a Nijeriya. Kasashe masu tasowa ma sun wuce wannnan gurin ballantana Nijeriya ‘UWAR AFRIKA’!

Haka nan kuma ba matsalar shugabanci ko jagoranci kadai za mu rika tattaunawa ba, a’a, hatta matsalarmu ta talakan Nijeriya, ita ma za mu rika tattauna ta a cikin wannan shafi naku, kamar matsalar rashin da’a, keta, hassada, kyashi, munafunci, sana’a, makotaka, dogaro da kai, bara, almajirci, karya doka, maula, tukin ganganci, rashin tarbiyya, shaye-shaye, dabanci da sauran abubuwa na matsaloli wadanda mu talakawa mu ka yi katutu a cikinsu.

Abin nufi a nan shi ne, a cikin wannan shafi za mu rika yiwa junanmu tsumagiyar kan hanya fyade yaro fyade babba!

Lallai wannan aiki na namu ba ne mu kadai. Aiki ne wanda hatta ku masu sauraro ku na da gudunmawar da ya wajaba ku bayar ta hanyar karfafa ma na gwiwa da bayyana ra’ayoyinku a cikin mutuntaka da sanin ya kamata.

Babban abinda ya kiamata mu gane shi ne, idan kasa ta cigaba kuma rayuawa ta inganta, sannan a ka samu yalwar arziki, to da nagari da mugu duka za su amfana da hakan. Watakila ma daga lokacin sai mugun ya gane cewa, babu sauran amfani a gare shi ci gaba da aikata muguntar, domin watakila a lokacin ba ya cikin fargabar da ta sanya shi aikata muguntar.

Misali a na shi ne, idan arziki ya yalwata, tattalin arziki ya bunkasa, kowa ya wadata, za ka tarar cewa cin hanci da rashawa ya na yin karanci, domin masu yin watakila su na yi ne saboda tsoron talauci. To, ka ga idan talaucin ya yi karanci kuma kowa ya san cewa ya na da kyakkyawar makoma, sai hankali ya kwanta a rage satar dukiyar al’umma.

To, kun ga ashe kenan shi kansa mugun, idan ya tsaya ya yi tunani da ‘MAHANGA’ mai kyau, zai ga cewa, ba kin sa mu ke yi ba, a’a, mu na so ne mu ga cewa, abinda ya ke son ya yi ya aikata shi kuma ya cimma burinsa ta hanya halastacciya. Idan kudi ka ke son samu, to ka samu na halak. Idan ’yanci ka ke nema, ka same shi ta hanyar doka. Wannan shi ne abinda ya dace kuma ya wajaba a dora kasar da ’yan kasar a kai bakidaya.

Hakika wannan babban aiki ne wanda ya shafi kowa. Mu kadai ba za mu iya ba, illa dai kawai za mu yi kokarin ganin mun bayar da tamu gudunmawar, amma tabbas LEADERSHIP A YAU LAHADI, ba za ta iya ita kadai ba. Ku ma sai kun taya mu, domin masu hikima su na cewa, hannu da yawa maganin kazamar miya!

Don haka mu na neman gudunmawar kowa da kowa. Akwai dama cikakkiya ga wanda ya turo da makala mai kyau da inganci, za mu buga ta a wannan shafi da yardarm Allah!

Ina mai tabbatar mu ku da cewa, bias yardarm Allah shi wanda zai kula da wannan shafi, wato Malam Musa, zai yi mu kiu jagoranci nagari cikin amana da ‘MAHANGA’ mai kyau.

A karshe Ina mai yi mu ku fatan alheri tare da rokon ku a kan ku saka ni cikin addu’o’inku a wannan sabon mukami da a ka dora mi ni alhakin kula da wannan jarida taku ta LEADERSHIP A YAU LAHADI. Hadiminku kuma Editanku, Nasir S. Gwangwazo. Bissalam!

SendShareTweetShare
Previous Post

SHARHIN GASAR PREMIER : ANYA KWALLIYA ZA TA BIYA KUDIN SABULU?

Next Post

Siyasar Kano: An Gano Dalilin Rikicin Sanata Gaya Da Kawu Sumaila

RelatedPosts

Za A Kawar Da Ta’addanci A Jihar Xinjiang Sakamakon Wadata Da Zaman Karko

Za A Kawar Da Ta’addanci A Jihar Xinjiang Sakamakon Wadata Da Zaman Karko

by Abdulaziz Kabir Muhammad
1 year ago
0

Babban gidan rediyo da talibijin na kasar Sin wato CMG...

Mun Yi Shiri Na Musamman Don Ceto Asibitin Koyarwa Na Jami’ar ABU Daga Durkushewa —Farfesa Ummdagas Ahmed

by Abdulaziz Kabir Muhammad
1 year ago
0

Asibitin koyarwa na jami’ar Ahmadu Bello (ABUTH) dake zariya na...

Tunawa Da Gwarzo Dakta Bala Yusuf Usman

Tunawa Da Gwarzo Dakta Bala Yusuf Usman

by Abdulaziz Kabir Muhammad
1 year ago
0

Wakilimu ya yi takaitaccen bincike a kan rayuwa da gudummawar...

Next Post

Siyasar Kano: An Gano Dalilin Rikicin Sanata Gaya Da Kawu Sumaila

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version