Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Sharhi

Bayan kotun koli ta tabbatar da nasarar zaben Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban Nijeriya, yanzu lokaci ya yi da shugaban kasar zai mayar da hankali wajen inganta gwamnatinsa ta yadda zai iya tunkarar matsaloli da ke fuskantar Nijeriya kamar yadda ya yi alkawari a lokacin yakin neman zabe.

Kwanaki sama da 50 kenan da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta goyi bayan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a kan ayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu shi ya yi nasara a zaben da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun 2023. Yayin da ita ma kotun koli a ranar Alhamis, 26 ga Oktoba ta tabbatar da wannan hukunci.

  • Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa
  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi

A hukuncin, alkalan kotun kolin su bakwai sun bayyana cewa wadanda suka shigar da kara sun gaza kawo kararan hujjoji da za su kore nasarar da Tinubu ya samu a zaben shugaban kasar.

Bayan watsi da kararrakin guda biyu da ‘yan takarar jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar da na LP, Mista Peter Obi suka shigar, kotun kolin ta tabbatar da hukuncin da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta yanke a ranar 6 ga watan Satumba, inda ta tabbatar da ayyana Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya.

Hukuncin da kotun koli ta yanke, ba wai kawai ya kawo karshen duk wasu kararraki da suka shafi zaben shugaban kasa ba, har ma da tabbatar da aikin shugaban kasa na tsawon shekaru hudu masu zuwa.

Ayyukan sun hada da samar da ingantacciyar shugabanci, samar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan Nijeriya wanda hakan ta sa aka cire tallafin man fetur da kuma dawo da darajar naira, wanda gwamnatin Tinubu ta fara tun daga farkon lamari.

Sai dai babban kalubalen da ke fuskantar ‘yan Nijeriya sun hada da rashin zaman lafiya, rashin samun ci gaba, ayyukan ‘yan bindiga da kuma cin hanci da rashawa.

Kamar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke cewa, “idan ba mu yaki ci hanci da rashawa ba, to zai kashe mu “. Cin hanci da rashawa kamar wutar daji ce da ke cin zukatan ‘yan Nijeriya. Babu wani bangare na rayuwar ‘yan Nijeriya da cin hanci bai dabaibaye ba.

Domin haka, dole ne gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali wajen karfafa yaki da cin hanci da rashawa. A lokacin yakin neman zabe, Tinubu ya yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin sake farfado da darajar Nijeriya.

Lallai idan har ‘yan Nijeriya za su ga sauyi, to dole ne Tinubu ya tashi tsaye wajen inganta gwamnatinsa da kuma yaki da cin hanci da rashawa a kowani bangare. Mafi yawancin mutane sun yi kara ga shugaban kasa ya yi kokarin gudanar da shugabanci nagari ta yadda zai iya farfado da darajar Nijeriya a idon duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Tsaro: Bai Wa Al’umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

Tsaro: Bai Wa Al'umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version