Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Shin Tinubu Zai Iya Kai Bantensa Bisa Yadda Ya Fara?

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Biyo bayan ganawar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi da hafsoshin tsaro a makon da ya gabata bayan hawansa mulki tare da karanta masu karatun-ta-natsu, miliyoyin ‘yan Nijeriya na fatan cewa za a samu gagarumin sauyi kan yanayin rashin tsaro tare dawo da Nijeriya cikin hayyacinta.

Tun bayan da aka rantsar da shi a matsayin zababben shugaban kasar Nijeriya na 16, Tinubu ya dai gaji tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari. Bayan rantsar da shi, wata tambaya daya ke ci gaba da yawo a zukatan ‘yan Nijeriya da dama shi ne, Shin ko Tinubu zai iya cika alkawarin da ya dauka na magance matsalar rashin tsaro da kasar nan ke fama da shi.

  • Jami’an Amurka Ba Za Su Iya Dakatar Da Matakan Sulhu Na Kasashen Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
  • Tinubu Zai Gana Da Zababbun Sanatoci A Gobe Alhamis

Bisa kididdigar kashe-kashen da aka yi a Nijeriya da wata cibiyar bincike ta Amurka ta fitar, ya nuna cewa an kashe akalla mutane 89,920 a Nijeriya sakamakon tashe-tashen hankula a cikin shekaru bakwai na farko na gwamnatin Buhari daga Mayu 2015 zuwa Mayu 2022.

Ita ma wata kungiya da ta sadaukar da kai wajen bin diddigin tashe-tashen hankula a Nijeriya ta fitar da rahotonta na shekarar 2023, wanda ya nuna cewa an kashe mutane 1,230 a kasar a rubu’in farko na shekarar 2023.

Rahoton ya kuma ce jami’an tsaro 79 ne suka mutu a cikin wannan lokaci, yayin da aka yi garkuwa da mutane 658 a fadin kasar.

ko bayan rantsar da Tinubu an ci gaba da kashe mutane tare da yin garkuwa da wasu da dama a cikin Nijeriya.

A daidai lokacin da Shugaba Tinubu ya hau kan karagar mulki, idanun ‘yan Nijeriya sun koma kansa tare da yi masa fatan alkairi na ganin ya magance kalubalen da ke gaban kasar nan, nusamman ma a bangaren tsaro. ‘Yan Nijeriya dai na sha’awar samar da kasa mai cike da tsaro, domin su samu nasarar yin barci da idanuwansu guda biyu ba tare da wata fargaba ba.

Bisa kudurinsa na magance tsaro, Tinubu ya yi ganawarsa ta farko da hafsoshin tsaron kasar nan, inda ya bayyana musu cewa bu sauran bayar da uzuri a bangaren jami’an tsaro.

Ya kuma bayyana musu cewa ba zai yarda da halin da al’ummar kasa ke ci gaba da raguwa ba. A cewar shugaban, a yanayin da yake ciki a halin yanzu, dole ne a hada kan tsaron kasa wajen ceto kasar nan.

Shugaban ya umarci hukumomin tsaro da su fito da wani tsari na magance matsalar rashin tsaro a Nijeriya. Ya ce ba shi da isasshen lokaci dole ne a gudanar da sauye-sauyen da suka dace da wuri-wuri.

Taron wanda shi ne na farko da hafsoshin tsaro, ya kasance karkashin jagorancin babban hafsan tsaro, Janar Lucky Irabor. Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Farouk Yahaya da babban hafsan sojin ruwa, Bice Admiral Awwal Gambo da shugaban hafsan sojan sama, Air Marshal Isiaka Amao da babban sufetan ‘yansanda, Usman Alkali Baba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
… A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

... A Makon Farkon Mulkin Tinubu, Mutum 78 Sun Mutu Tare Da Garkuwa Da 12

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version