Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Wutar Olympics Na Haskaka Duniya Duk Da Duhun Da Ake Ciki

by
4 months ago
in DAGA BIRNIN SIN
3 min read
Sharhi: Wutar Olympics Na Haskaka Duniya Duk Da Duhun Da Ake Ciki
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Lubabatu Lei,

Samuel Ikpefan, shi ne dan wasan tseren yada kanin wani na dusar kankara na farko a Nijeriya, haka kuma dan wasan tseren dusar kankara na farko da ya shiga gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu a tarihin kasar. Yanzu haka, yana kokarin share fagen gasar Olympics na lokacin hunturu da nan ba da jimawa ba za a kaddamar a birnin Beijing. Idan ba a manta ba, yau shekaru hudu ke nan da suka wuce, tawagar Nijeriya da ke kunshe da ‘yan wasa mata uku ta halarci gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu na birnin Pyeongchang, karon farko da ‘yan wasan Nijeriya suka halarci gasar ta lokacin hunturu.

Samuel ya ce, yadda ‘yan wasan Nijeriya suka halarci gasar a shekaru hudu da suka wuce a birnin Pyeongchang yana da muhimmiyar ma’ana, haka kuma ya karfafa masa gwiwa da ma sauran al’ummar Afirka.

Labarai Masu Nasaba

Yau Ake Cika Shekaru Hudu Da Kafa Kwamitin Kula Da Harkokin Waje Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

Kasashen BRICS Sun Yi Kira A Hada Kai Don Tinkarar Sauyin Yanayi

Sakamakon yanayi mai dumi, akasarin kasashen Afirka ba su samu ci gaba sosai ba a wasannin kankara. Daga cikin kasashen Afirka 54, 15 ne kawai suka taba shiga gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu, sai dai hakan ba zai iya hana ‘yan wasa na kasashen Afirka ba, wadanda ba su son a bar su baya.

Ban da ‘yan wasa, kasashe daban daban na kara zura ido ga gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu na Beijing, wadanda suke fatan ganin gasar ta taimaka ga daidaita sabani da ma karfafa fahimtar juna da zumunci a tsakanin kasashe daban daban, musamman a lokacin da ake fuskantar koma bayan tattalin arziki a sakamakon annobar Covid-19 da ke addabar duniya da ma kalubale na nuna bangaranci da ma fin karfi.

A ranar 25 ga wata, shugaban tarayyar Nijeriya, Muhammadu Buhari ya bayar da sanarwa, inda ya jaddada goyon bayansa ga gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu da za a gudanar a birnin Beijing. Ya ce, gasar wasannin Olympics dandali ne na karfafa zumunci da hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa, ya kuma yi fatan dukkan wasannin za su cimma burikan da ake fatan cimmawa na Olympics wajen daga matsayin ruhin wasanni, da karfafa zumunci, da kuma mutunta juna. Shi ma ministan harkokin wajen kasar Madagascar, Patrick Rajoelina, ya bayyana a kwanan baya cewa, wasannin Olympic tamkar wata muhimmiyar hanya ce ta daga matsayin hadin kan kasa da kasa. “Ta hanyar mutunta ruhin Olympic, za mu iya cimma nasarar hada mutane wuri guda ta hanyar kyakkyawar fahimtar juna da hadin kan kasa da kasa.”

Mutane da yawa daga kasashen Afirka sun bayyana adawarsu game da yadda wasu kasashe kalilan suke neman siyasantar da gasar don cimma burinsu na siyasa. Shugaban kwamitin shirya gasar wasannin Olympics na kasar Zimbabwe Thabani Gonye, ya yi kakkausar suka kan yadda ake siyasantar da harkokin wasanni. Yana mai cewa, ba za a iya hada wasanni da siyasa ba. Ya kamata kasashen da abin ya shafa su mai da hankali a kan ‘yan wasansu, don taimaka musu cimma nasara a wajen gasar. Ya kara da cewa, ko da yake bai samu damar zuwa wajen gasar ba, amma shi da abokansa za su kasance a gaban talabijin, don karfafawa ‘yan wasan gwiwa.

Sanin kowa ne cewa, a cikin shekaru biyu da suka wuce, tattalin arzikin duniya ya dakushe a sakamakon annobar Covid-19, tare da haifar da rufe wa juna kofa da kawo baraka a tsakanin kasa da kasa. A sa’i daya, yadda wasu ‘yan siyasar kasashen yamma suka yi ta haifar da fito-na-fito a tsakanin kasa da kasa, ya kara tsananta halin da ake ciki. Wannan ya sa, a gasar wasannin Olympics na Tokyo da aka gudanar a bara, an kara saka kalmar “Together” cikin taken gasar Olympics, don ta zama “Faster Higher Stronger da ma Together”, wanda ya bayyana bukatun al’ummar duniya na karfafa hadin kansu don fuskantar kalubale.

Ruhin wasannin Olympics na bayyana cewa, duk irin kalubale da ake fuskanta, hadin kai shi ne babban makami ga dan Adam.

A shekaru hudu da suka gabata, shugaban kwamitin wasannin Olympics na kasar Nijeriya, Habu Gumel ya bayyana cewa, wannan shi ne karo na farko da kasar Nijeriya ke halartar gasar wasannin Olympics na lokacin hunturu, amma ba zai zama na karshe ba. Ya ce, “A gasar wasannin Olympics na Beijing, za mu ga sauye-sauye, ba kawai ta fannin wasannin da za mu halarta ba, har ma za mu samu karin ci gaba.” Yanzu haka, ‘yan wasa na kasashen Afirka suna kokarin share fagen gasar tare da takwarorinsu na sauran kasashen duniya, mu ma muna musu fatan cimma nasarori, muna kuma fatan su isar da sakon hadin kai ga al’ummun kasashen duniya.

Shugaban kwamitin wasannin Olympics na kasa da kasa, Thomas Bach ya ce, “Duk duhun da muka shiga, wutar wasannin Olympics za ta haskaka mana hanya don mu ga karshenta”. Nan da mako guda, za mu hadu a gasar wasannin Olympics, inda za mu rungumi makomarmu tare!

 

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Tanzania Ta Karbi Karin Tallafin Rigakafin COVID-19 Daga Kasar Sin

Next Post

Me Kuka Sani Game Da Bikin Bazara Da Nune-nunen Fitilu Na Gargajiyar Kasar Sin?

Labarai Masu Nasaba

Yau Ake Cika Shekaru Hudu Da Kafa Kwamitin Kula Da Harkokin Waje Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

Yau Ake Cika Shekaru Hudu Da Kafa Kwamitin Kula Da Harkokin Waje Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

by CMG Hausa
16 hours ago
0

...

Kasashen BRICS Sun Yi Kira A Hada Kai Don Tinkarar Sauyin Yanayi

Kasashen BRICS Sun Yi Kira A Hada Kai Don Tinkarar Sauyin Yanayi

by CMG Hausa
17 hours ago
0

...

Al’ummar Afirka Ba Su Bukatar A Yi Musu Lacca

Al’ummar Afirka Ba Su Bukatar A Yi Musu Lacca

by CMG Hausa
19 hours ago
0

...

Masana sun yi Allah wadai da yunkurin Amurka na neman dakile cigaban al’ummar Xinjiang

Masana sun yi Allah wadai da yunkurin Amurka na neman dakile cigaban al’ummar Xinjiang

by CMG Hausa
20 hours ago
0

...

Next Post

Me Kuka Sani Game Da Bikin Bazara Da Nune-nunen Fitilu Na Gargajiyar Kasar Sin?

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: