Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

An Shawarci Al’ummar Hausawa Kan Su Rungumi Jaridun Hausa

by Tayo Adelaja
September 12, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Balarabe Abdullahi, Zariya

Wani mai kishin harshen Hausa, kuma dan kasuwa a Zariya, mai suna Alhaji Hashimu Mai kashu, ya bayyana matukar damuwarsa da yadda mafiya yawan al’ummar Hausawa ba su damu da sayen jaridun da ake buga su da harshen Hausa ba, sai dai jaridun Ingilishi suka fi mayar da hankalinsu a kai, Alhaji Hashimu mai kashu ya bayyana hakan ne jim kadan bayan wata jarida mai suna TASKIRA ta karrama shi a Zariya, kan ayyukan tallafa wa al’umma da yake yi a sassan Zariya da kewaye.

A cewar Mai kashu, yadda jaridun Hausa ke fito wa  irin fitowar murucin kan dutse, amma, in ji shi,sai a wayi gari ba su, ba alamunsu, a dalilin sakaci da rashin kishin Hausawa musamman manyan ‘yanboko da kuma masu hannu da shuni.

Alhaji Hashimu,wanda kuma shi ne tsohon shugaban ‘yan kasuwar Dan-magaji a Zariya, ya ce lokaci ya yi da ‘yankasuwa da manyan ‘yanboko za su rika bayar da tallace-tallacensu a jaridun Hausa, domin masu buga jaridun su samu saukin fuskantar matsalolin da suke fuskantar matsalar rashin kudi, a duk lokacin da suka tashi buga jaridun na su.

Da ya juya ga ma su jagorantar al’umma, tun daga kananan hukumomi zuwa jihohin da suke Arewacin Nijeriya, sai ya shawarce su da su rika amfani da jaridun Hausa wajen sanar da jama’arsu abubuwan da suke yi musu, da kuma abubuwan da suke bukata al’ummomin da suke mulkarsu su yi musu.

Ga jaridun kuwa ya nuna matukar gamsuwarsa da yadda wasu ke mayar da hankalinsu ga labaran da suka shafi masu karanta jaridun. Ya ce wannan na daga cikin dalilan da suka sa a duk lokacin da jaridun suka fito, masu sayen jaridun ke daukar jaridun tamkar mahadin Karin-karin kumallo a garesu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Bauchi Za Ta Hukunta Manyan Ma’aikata A Kan Rashin Zuwa Aiki

Next Post

Cikin Watanni Bakwai Hukumar Kwastan Ta Tara Miliyoyi A Adamawa

RelatedPosts

Tallafin Gwamnatin Kaduna

Rikita-rikitar Korar Ma’aikata a Kaduna: Ba A Zabe Ni Don Biyan Albashi Ba – el-Rufai

by Sulaiman Ibrahim
3 hours ago
0

Daga Ibrahim Ibrahim Da Shehu Yahaya, Kaduna. …Ba Da Jimawa...

Gbajabiamila

Gbajabiamila Ya Zargi Jihohi Kan Tabbatar Da ‘Yancin Kananan Hukumomi

by Sulaiman Ibrahim
4 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Abuja Shugaban majalisar wakilai, Honarabul Femi...

Ramadan: Sarkin Karaye Ya Yi Kiran Tausaya Wa Talaka 

Ramadan: Sarkin Karaye Ya Yi Kiran Tausaya Wa Talaka 

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kano   Mai Martaba Sarkin karaye...

Next Post

Cikin Watanni Bakwai Hukumar Kwastan Ta Tara Miliyoyi A Adamawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version