Shekara 10 Da Sace ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bayyana Abubuwan Alhini
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara 10 Da Sace ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bayyana Abubuwan Alhini

byYusuf Shuaibu
1 year ago
Chibok

Shekara 10 kenan da sace ‘yan mata 276 na makarantar sakandaren gwamnati da ke garin Chibok a Jihar Borno, an fitar da wani sabon rahoto da ke nuna cewa ‘yan mata 21 daga cikin wadanda aka sako ya zuwa yanzu sun dawo gida tare da yara 34.

Wannan yana cikin rahoton da Gidauniyar Murtala Muhammed (MMF) ta fitar ta kuma ta raba wa manema labarai a karshen mako a Abuja.

  • Bangaren Amurka Ya Mayar Wa Bangaren Sin Da Kayayyakin Tarihi 38 Da Suka Bata Daga Sin
  • Shari’ar Zargin Karkatar Da Dukiyar Al’umma: Ganduje Da Iyalansa Ba Su Halarci Kotu Ba

Kamar yadda gidauniyar ta ce, rahoton an yi shi ne domin tunawa da cika shakara 10 da sace ‘yan matan. Rahoton ya kuma tabbatar da cin zarafi da auren dole da ‘yan matan suka fuskanta a lokacin da suke tsare a hannun ‘yan ta’addan.

Haka kuma rahoton na gidauniyar ya kara bayyana cewa iyayen daliban aka sace su 48 ne suka mutu. Sauran iyayen daliban da ke raye kuma na rayuwa cikin tashin hankali da fargabar rashin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki.

Babban Daraktan gidauniyar MMF, Dakta Aisha Muhammad-Oyebode wacce ta gabatar da rahoton ta bayyana cewa, gidauniyar ta lissafa wasu muhimman shawarwari guda 10.

Gidauniyar ta ce ya kamata gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da kasashen duniya su ba da fifiko a kan wadannan shawarwari. Shawarwarin sun hada da, daukar ingantattun matakan tsaro, shirye-shiryen tallafa wa kuyuka da tsarin ankararwa cikin gaggawa dangane da barazanar tsaro.

Ta ce, “A cikin shekara 10 tun lokacin da aka yi garkuwa da ‘yan matan Chibok ya janyo fusata al’ummar duniya gaba daya, kowani al’amari ya sauya a Nijeriya, inda masu garkuwa da mutane ke ci gaba da cin karansu babu babbaka na tsawon shekaru masu yawa.

“A daidai lokacin da Nijeriya ke fama da annoban garkuwa da mutane wanda ba ta nuna alaman raguwa ba, muna kira ga hukumomin Nijeriya da na kasa da kasa su dauki muhimman matakai domin magance abubuwan da ke janyo rikice-rikice da tashin hankali kan mata, wadanda suka hada da fatara, rashin natsuwa da tabarbarewar tattalin arziki.

“Rahoton ya gano cewa cikin 91 na daliban makarantar guda 276 har yanzu ba su san inda aka dosa ba.

“Rahoton ya kuma bayyana cewa ‘yan matan Chibok 21 da aka sako sun samu sun dawo da yara 34, wanda ya nuna sun fuskanci cin zarafi na jin jima’I da su da kuma tilasta musu yin auren dole lokacin da suke tsare.

“Rahoton MMF ya bayar da shawarar cewa a yi kokarin magance tushen yin garkuwa da mutane, sannan ya bukaci karfafa hadin gwiwa na kasa da kasa wajen daukar matakan kawo karshen lamarin.”

Ta kuma bayar da shawarar a dauki matakin tabbatar da hukunta wadanda ke da hannu kan wannan mummunan labari komin matsayin da suke da shi doka ta yi aiki a kan kowa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Likitocin Kasar Sin Sun Taimakawa Al’ummun Saliyo Da Dabarun Yaki Da Malaria

Likitocin Kasar Sin Sun Taimakawa Al’ummun Saliyo Da Dabarun Yaki Da Malaria

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version