Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai - Janar Musa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekaru 60: DICON Ta Taimaka Wajen Samar Mana Da Makamai – Janar Musa

bySadiq
1 year ago
DICON

Babban Hafsan rundunar tsaron Nijeriya, Janar Christopher Gwabin Musa, ya bayyana cewa ma’aikatar sarrarafa makamai ta Nijeriya (DICON), ta taimaka wajen samar wa rundunar kayayyakin aiki.

Kayayyakin sun sun hada da motocin yaki da kayayyakin sulken da rundunar soji ke bukata na aikin samar da tsaro a kasar.

  • Birtaniya Za Ta Wahala Idan Likitocin Nijeriya Suka Bar Kasar – Ministan Lafiya
  • Ban Taɓa Karɓar Cin Hanci Ko Taɓa Ƙuɗin Ƙananan Hukumomi Ba – Shekarau

Janar Musa, ya bayyana hakan ne, a taron kwanaki biyu da aka soma yau a Abuja na cikar ma’aikatar ta DICON shekaru 60 da kafuwa.

Nasarorin da ma’aikatar ta samu ba ya rasa nasaba da sanya hannu kan dokar ma’aikatar ta shekarar 2023 da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu a kai a watan Nuwamban 2023.

Idan ba a manta ba, ya bai wa ma’aikatar damar cimma manyan nasarori gami da fadada ayyukanta domin ci gaban Nijeriya.

Tun da fari dai, Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa assasa ma’aikatar sarrafa makaman a shekarar 1964 alamu ne na cin gashin-kai da Nijeriya ta tabbatar, wajen harkokin tsaro da ci gaban kasa.

Ma’aikatar ta zama silar nasarar ayyukan tsaro a kasar tare da fara sayar wa kasashen ketare makamai.

A shekarun da ta kwashe, ma’aikatar ta yi namijin kokari wajen shimfida kyakkyawar manhajar samar da tsaro a kasar.

Sannan ta taimaka wa rundunar tsaron Nujeriya da kayayyaki, domin saukaka ayyukansu na tsaro.

Ministan, ya bayyana cewa ko shakka babu, a karkashin mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ma’aikatar za ta ci gaba da samar da nasarori a wannan fannin tsaro.

A nasa jawabinsa, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya wakilta, ya ce shekaru 60 da kafuwar ma’aikatar sarrafa makamai alamu ne na tabbatar da tsantsar kishin kasa a harkar tsaro.

Shekaru 60 da suka gabata, ma’aikatar DICON ta himmatu ne, wajen sarrafa makamai da kayan yaki domin taimaka wa rundunar tsaro da sauran ma’aikatun tsaron Nijeriya a kokarinsu na wanzar da zaman lafiya a kasa baki daya.

Shugaban ya ce, hakika ma’aikatar DICON ta taka muhimmiyar rawa a samar wa dakarun Nijeriya da kayan aiki a lokacin yakin basasa domin tabbatar da kasantuwar Nijeriya kasa daya mai cin gashin-kanta.

Shugaba Tinubu, ya kara yin kira ga jagororin ma’aikatar da su kara himma da fadada tunani ga samar da kayayyakin zamani a shirin gwamnati na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar kasar nan.

Har wa yau, ya yi kira ga ‘yan kasa su taimaka su bayar da goyon baya ga nasarar ma’aikatar.

Daga bisani, shugaban ya kaddamar da sabon tambarin ma’aikatar tare da littafi na musamman da aka wallafa na cikar DICON shekaru 60 da kafuwa.

Taron, ya samu halartar ministoci, shugabannin tsaro da jami’an kasashen waje da kamfanoni da manazarta harkokin tsaro da ‘yan jarida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

WATA SABUWA: Ganduje Ya Nuna Rashin Jin Daɗi Bayan Tinubu Ya Masa Tayin Muƙamin Jakada

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version