Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Shettima Ya Ja Kunnen El-Rufai: Hawainiyarka Ta Kiyayi Ramarmu

by Tayo Adelaja
October 1, 2017
in LABARAI, MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba, Kaduna

Shugaban gamayyar kungiyoyin matasan Arewa (CNG), Alhaji Shettima Yerima, ya ja kunnen gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmed El-Rufai, ya na mai cewa hawainiyarsa ta kiyayi matasan Arewa, inda bayyana cewar, ya na wasa da wuta ne a kan cewar da ya yi a cafko ’ya’yan kungiyar da su ka baiwa ‘yan kabilar Igbo wa’adin daya ga watan Oktobar shekarar 2017 su gaggautawa ficewa daga yankin Arewa.

Yerima, wanda ya na maida martani ne a kan takardar da gwamnan ya ce ya karbo daga kotu don cafko su, ya ce, yunkurin na gwamnan ya nuna a zahiri shi makiyin gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari ne.

Ya ce, kodayake kungiyar ba ta son yin wata jayayya da gwamnan, domin a yanzu abin da ke gabanta shi ne ganin an gina kasar nan. “Watakila gwaman yana kokarin karkatar da hankalin gwamnati ne, mu kuma ba za mu yarda da a yi amfani da mu ba wajen hakan,” in ji shi.

Game da batun kamo su kuwa, Shugaban kungiyar cewa ya yi “ba a ba mu sammaci ba, kuma in an ba mu za mu gurfana, domin kuwa ba mu fi karfin doka ba.”

Ya yi ikirarin cewa, “ba inda za mu gudu saboda barazanar El-Rufai, domin mu ba matsorata ba ne. ‘Yan kasar nan su ne za su yi alkalanci don gano ko el-rufai dan kasar nan ne na asali, kuma mai son zaman lafiya a kasar nan?”

Da a ka tambaye shi akan sanarwar da Atoni Janar na kasa, Abubakar Malami ya fitar kwanan baya, inda ya ce ba za a kama ‘ya’yan kungiyar ba saboda yanayi na tsaro a kasa, Yeriman ya bayyana cewa, abin da El-rufai ke nufin yi, yana son ya janyo hatsaniya ne kawai a kasar nan.

Ita ma a nata bangaren, kungiyar tuntuba ta Arewa, ACF gargadi ta yi da a kiyaye duk wani abu da zai yi wa zaman lafiya zagon kasa. Sakatare Janar na kungiyar, Mista Anthony Sani, ya bayyana cewar, karbo takardar da gwamnatin jihar Kaduna ta ce ta yi daga kotu don cafko ‘ya’yan kungiyar gamayyar matasan Arewar ba wani abin dole ba ne, illa neman fitina.

Sani ya yi nuni da cewa, karbo takardar zai janyo koma-baya akan kokarin da Gwamnonin Arewa ke yi na tabbatar da zaman lafiya, bayan da Gwamnonin suka umarci matasan su janye wa’adin, kuma suka janye.

A cewarsa, “ni ma na bi ra’ayin wadanda suke cewa karbo takardar ba wani abu ne na dole ba, tunda gamayyar kungiyoyin tuni sun janye wa’adin. Karbo takardar zai janyo rusa kokarin kawo zaman lafiyar da Gwamanonin Arewa suke yi karkashin jagorancin Gwaman Jihar Borno, kuma Shugaban kungiyar Gwamanonin Arewa, Kashim Shettima, da kuma kwamitin zaman lafiya da tsohon Shugaban kasa Janar Abubakar Abdulsalami mai ritaya ke yi, ba lallai ba ne sai gwamnati ta karbo takardar ta kama matasan ba daga Kotu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Labarin Bawa Dorugu: Bahaushen Farko Da Ya Fara Zagaya Turai

Next Post

Akwai Bukatar Nutsuwa A Gyaran Fasalin Nijeriya – Tanko Yakasai

RelatedPosts

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim An yi wa Shugaba Muhammadu Buhari da...

Allurar Rigakafin

An Fara Yin Allurar Riga-kafin Korona a Nijeriya

by Muhammad
7 hours ago
0

Yau Ake Sa Ran Buhari Da Osinbajo Za Su Karbi...

Mukabalar

Kotu Ta Dakatar Da Yin Mukabalar Sheikh Abduljabbar Da Malaman Kano.

by Muhammad
7 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Wata kotu a Jihar Kano ta...

Next Post

Akwai Bukatar Nutsuwa A Gyaran Fasalin Nijeriya – Tanko Yakasai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version