CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Shin Scott Morrison Da Irinsa Suna Sokar Kasar Sin Ne Don Samun Kudi Daga Kasar Ta Sin?

by CRI Hausa
December 4, 2020
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Shin Scott Morrison Da Irinsa Suna Sokar Kasar Sin Ne Don Samun Kudi Daga Kasar Ta Sin?
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

In an ambato ’yan siyasan kasa da kasa da suke saurin canza ra’ayi, ba za a taba mantawa da firaministan kasar Australiya Scott Morrison. Kwanan baya, ya bukaci kasar Sin ta nemi gafara daga wajen kasarsa dangane da wani zanen da kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya wallafa a shafinsa na Tiwitter game da yadda sojojin Australiya suka aikata ta’asa a kasar Afghanistan. Amma jiya Alhamis ya sauya ra’ayinsa ba zato ba tsammani, inda ya yi shelar cewa, yana fatan tuntubar kasar Sin ta hanyar da ta dace. A cewarsa, huldar da ke tsakanin Australiya da Sin suna kawo moriyar juna tsakanin kasashen 2.

Yayin da ya shafa wa kasar Sin kashin kaji, mista Morrison yana kuma yunkurin neman samun kudi ne daga kasar Sin. Ko ya haukace ne? A cikin shekaru 2 ko fiye da haka da suka wuce bayan da ya zama firaministan Australiya, ya bi sahun kasar Amurka ta fuskar siyasa, inda ya rika sukar kasar Sin. Amma yana kokarin cin gajiyar bunkasuwar kasar Sin ta fuskar tattalin arziki. Sanin kowa ne cewa, mista Morrison ya yi dabara domin samun moriyar siyasa. Dalilin da ya sa haka shi ne domin wannan dan siyasa mai taurin kai kuma mai tunanin yakin cacar baki yana kallon kasar Sin bisa tunaninsa, yana kuma kokarin faranta ran Amurka, a yunkurin samun moriyar siyasa.
Idan mista Morrison yana son ya samu kasarsa da kasar Sin su amfana, to, ya kamata ya nuna sahihanci tukuna. Dole ne ya fahimci cewa, kasarsa ta Australiya ba ta da muhimmanci ko kadan yayin da wasu kasashen yammacin duniya suke yunkurin dakatar da ci gaban kasar Sin. Za kuma ta dandana kudarta idan ya bi umurnin wasu a nahiyar Asiya da yankin tekun Pasific. Jama’ar Sin ba za su yarda da yadda wasu suke cin gajiyar ci gaban kasarsu, tare da yunkurin dakatar da bunkasuwar kasar Sin ba. Mista Morrison da sauran irinsa, ba za su taba cimma burinsu ba! (Tasallah Yuan)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Sin Ta Yi Nasarar Tashi Saman Na’urar Bincike A Waje Da Doron Duniya

Next Post

Shugaban Kasar Sin Ya Sanar Da Gagarumar Nasarar Da Kasarsa Ta Samu A Yaki Da Talauci

RelatedPosts

Shugaba Xi Ya Duba Shirye-shiryen Da Ake Yi Na Karbar Bakuncin Gasar Olympic Ta Birnin Beijing A 2022

Shugaba Xi Ya Duba Shirye-shiryen Da Ake Yi Na Karbar Bakuncin Gasar Olympic Ta Birnin Beijing A 2022

by CRI Hausa
4 hours ago
0

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya duba shirye shiryen da...

Adadin Wayoyin Hannu Masu Fasahar 5G Da Sin Ta Fitar Ya Kai Miliyan 163 A Shekarar 2020

Adadin Wayoyin Hannu Masu Fasahar 5G Da Sin Ta Fitar Ya Kai Miliyan 163 A Shekarar 2020

by CRI Hausa
5 hours ago
0

Sabbin alkaluman cibiyar nazarin fasahar sadarwa ta kasar Sin CAICT...

GDPn Kasar Sin Ya Karu Da Kaso 2.3 A Shekarar 2020

GDPn Kasar Sin Ya Karu Da Kaso 2.3 A Shekarar 2020

by CRI Hausa
5 hours ago
0

Wasu alkaluma da hukumar kididdigar kasar Sin (NBS) ta fitar...

Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Sanar Da Gagarumar Nasarar Da Kasarsa Ta Samu A Yaki Da Talauci

Shugaban Kasar Sin Ya Sanar Da Gagarumar Nasarar Da Kasarsa Ta Samu A Yaki Da Talauci

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version