Shirin X Space Na LEADERSHIP: Tabbas Gwamnatin Kano Ta Hau Turbar Bunkasa Ilimi – Mahalarta
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin X Space Na LEADERSHIP: Tabbas Gwamnatin Kano Ta Hau Turbar Bunkasa Ilimi – Mahalarta

byNaziru Adam Ibrahim
1 year ago
Kano

Masu ruwa da tsaki a fannin ilimi sun yaba wa kokarin Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, wajen inganta bangaren duba da gagarumar nasarar da ake samu biyo bayan ayyana dokar ta baci da ya yi a fannin ilimin jihar.

Sun bayyana hakan ne cikin shirin tattaunawa da LEADERSHIP ta shirya a shafinta na X da akafi sani da twitter inda masu ruwa da tsakin suka yaba da da matakan da gwamnatin ke dauka.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Birnin Baoji Na Lardin Shaanxi Da Birnin Tianshui Na Lardin Gansu

Cikin jawabinta, babbar hadimar Gwamna Abba Kabir Yusuf, kan ilimin Mata  Hajiya Yesmin Mukhtar, ta ce gwamnan ya gyara makarantu da dama da ke cikin halin kaka-ni-ka-yi tare da bude wasu da a da can baya an nuna musu halin ko in kula.

Sauran ci gaban da aka samu kamar yadda sauran masu tofa albarkacin bakinsu irin su tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Farfesa Usman Moddibo da mai mallakar shafin Arewa Twitter, Malam Abdullahi Nasarawa suka bayyana, akwai kaddamar da manyan ayyuka na gyaran makarantu da kuma inganta kwazazon malamai.

Duk sun yaba wa gwamnatin jihar kan wasu daga cikin jiga-jigan kokarinta na inganta harkar ilimin irin su ware kaso 29 na kasafin jihar ga bangaren ilimi da diban malamai fiye da 5,600 da biyan kudaden jarrabawar WAEC da NECO ga dalibai da bude cibiyoyin samun ilimin zamani na na’ura mai kwakwalwa.

Sai dai sun ce duk da haka akwai sauran aiki a gaba wanda idan aka mayar da hankali tabbas za a yi nasarar har karshe.

Shi ma kwamishinan ilimi na Jihar Kano, Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana bukatar yaba kokarin da gwamnatin ke yi ta hanyar ba ta duk wani hadin kai da take bukata don samun nasara.

Zuwa yanzu dai, daga cikin gagarumin kokarin da take yi, Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta fitar da fiye da Naira Biliyan 2.7 domin gina ajujuwa 176 da ofisoshi 88 a sassan kananan hukumomin jihar 44.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Tare Hanyar Zamfara, Sun Sace Matafiya 150

Ƴan Bindiga Sun Tare Hanyar Zamfara, Sun Sace Matafiya 150

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version