Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home DAGA BIRNIN SIN

Shirin Ziri Daya Da Hanya Daya Zai Taimakawa Mutane Miliyan 7.6 Na Kasashen Da Ya Ratsa Su Fito Daga Kangin Talauci

by Sulaiman Ibrahim
April 6, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Shirin Ziri Daya Da Hanya Daya Zai Taimakawa Mutane Miliyan 7.6 Na Kasashen Da Ya Ratsa Su Fito Daga Kangin Talauci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga CRI Hausa

Yau Talata, ofishin yada bayanai na majalissar gudanarwar kasar Sin, ya fitar da takardar bayani game da aikin da gwamnati ke yi na rage talauci a kasar. Takardar na nuna cewa, kasar Sin tana son shiga shirin rage talauci na kasa da kasa, domin zurfafa muamalar kasa da kasa kan aikin. Bankin duniya ya kuma fidda wani rahoto dake cewa, shirin ziri daya da hanya daya da kasar Sin ta fidda, zai taimakawa mutane miliyan 7.6 na kasashen da shirin ya ratsa su fito daga kangin talauci, da kuma fitar da mutane miliyan 32 daga matsakacin talauci.
Cikin takardar, an kuma bayyana cewa, bayan kafuwar Jamhuriyyar Jamaar kasar Sin, ya zuwa yanzu, shekaru 70 da suka wuce, cikin wadannan shekaru 70, kasar Sin ta ba da taimako iri daban daban ga kasashe da kungiyoyi sama da 160, dake yankunan Asiya, da Afirka, da Latin Amurka, da Caribbean, da nahiyar Oceania da kuma Turai da sauransu, ta yadda, kasashe masu tasowa za su cimma burin neman ci gaba da MDD ta tsara.
A sai daya kuma, kasar Sin ta yi hadin gwiwa da kasa da kasa wajen tsara shirye-shiryen rage talauci. A nahiyar Afirka, Sin ta ba da taimako ga kasashen nahiyar wajen gina ababen more rayuwa, da makarantun ba da horo, da kuma gina gidaje da sauransu, ta kuma kafa yankunan hadin gwiwar aikin gona, domin inganta hadin gwiwar fasahohin gona. Ban da haka kuma, Sin ta kuma kafa asibitin zumunci na Sin da Afirka, da hedkwatar rigakafin cututtuka ta Afirka da dai sauran makamantansu.
Bugu da kari, kasar Sin ta kafa wasu dandali, da shirya wasu darussan horaswa domin musayar raayoyi da fasahohi wajen rage talauci. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

SendShareTweetShare
Previous Post

Kasar Sin Tana Hadin Gwiwa Tare Da Sauran Kasashe A Fannin Samar Da Allurar Rigakacin COVID-19

Next Post

Sin: Har Yanzu Xinjiang Na Fuskantar Barazanar Ta’addanci Da Tsattsauran Ra’ayi Duk Da Rashin Kai Wani Hari Cikin Shekaru 4

RelatedPosts

Tsohon Ministan Kudin Girka: Jari Da Sin Ke Zubawa A Afirka Ya Zamo Muhimmin Tallafi Sama Da Mulkin Mallaka Da Kasashen Yamma Suka Yi A Nahiyar

Tsohon Ministan Kudin Girka: Jari Da Sin Ke Zubawa A Afirka Ya Zamo Muhimmin Tallafi Sama Da Mulkin Mallaka Da Kasashen Yamma Suka Yi A Nahiyar

by Sulaiman Ibrahim
7 hours ago
0

Daga CRI Hausa Tsohon ministan kudin kasar Girka Yanis Varoufakis,...

Ya Kamata Nahiyar Afrika Ta Dauki Darasi Daga Annobar COVID-19

Ya Kamata Nahiyar Afrika Ta Dauki Darasi Daga Annobar COVID-19

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Fa’iza Mustapha Har yanzu duniya na ci gaba da...

Manufar Wariyar Launin Fata Ta Amurka Na Keta Hakkin Dan Adam

by Sulaiman Ibrahim
13 hours ago
0

Daga CRI Hausa A shekarar 1962, marubucin kasar Amurka, ‘dan...

Next Post
Sin: Har Yanzu Xinjiang Na Fuskantar Barazanar Ta’addanci Da Tsattsauran Ra’ayi Duk Da Rashin Kai Wani Hari Cikin Shekaru 4

Sin: Har Yanzu Xinjiang Na Fuskantar Barazanar Ta’addanci Da Tsattsauran Ra’ayi Duk Da Rashin Kai Wani Hari Cikin Shekaru 4

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version