Shugaba Tinubu Ya Umurci A Tabbatar Da Daƙile Masu Haƙar Ma'adanai Ba Bisa Ƙa'ida Ba
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Tinubu Ya Umurci A Tabbatar Da Daƙile Masu Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya umurci hukumomin tsaro da su ƙara kaimi wajen daƙile ayyukan haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba a faɗin Nijeriya. Shugaban ya ba da wannan umarni ne yayin wani taro a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, inda mahalarta kwas na 32 na Kwalejin tsaro ta ƙasa (NDC) suka tattauna kan damarmamakin da ke cikin sashen hakar ma’adinai wajen tallafawa tsaro da ci gaban ƙasa.

Tinubu ya jaddada muhimmancin samun hanyoyin tattalin arziki da dama, tare da nuna buƙatar kamfanonin haƙar ma’adinai su ba da fifiko ga lafiyar ƴan Nijeriya, musamman mazaunan wuraren da ake gudanar da ayyukan hakar.

  • Fiye da Mata 50 Masu Haƙar Ma’adinai Sun Fuskanci Cin Zarafi a Jihar Nasarawa
  • Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba: Nijeriya Na Asarar Naira Biliyan 9 Duk Shekara – Majalisa

Shugaban ya yaba wa mahalarta NDC kan binciken su mai zurfi, tare da lura da fahimtar su game da tasirin masana’antar haƙar ma’adinai ga zaman lafiyar ƙasa. Ya amince da ƙalubalen da haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba ke kawo wa, inda ya bayyana su a matsayin barazana da dole ne hukumomin tsaro su magance cikin gaggawa.

Tinubu ya kuma tabbatar wa tawagar goyon bayan gwamnatinsa wajen kammala ginin helkwatar NDC a Abuja, don ƙarfafa rawar da wannan cibiya ke takawa wajen tsara dabarun tsaron Nijeriya.

Kwamandan NDC, Rear Admiral Olumuyiwa Olotu, ya yaba da goyon bayan Shugaban ga kwalejin, tare da bayyana muhimman ayyukan ci gaba da aka samu a ƙarƙashin mulkinsa. Ya kuma nemi taimako wajen kammala ginin rukunin NDC na dindindin, wanda aka samu jinkirin kammala shi tun daga shekarar 2010.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Hukumar Yaki Da Shan Maganin Kara Kuzari Yayin Wasanni Ta Duniya Ta Fallasa Ayyukan Amurka Game Da ’Yan Wasa Masu Keta Ka’idoji

Hukumar Yaki Da Shan Maganin Kara Kuzari Yayin Wasanni Ta Duniya Ta Fallasa Ayyukan Amurka Game Da ’Yan Wasa Masu Keta Ka’idoji

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version