Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wang Yi
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wang Yi

byCGTN Hausa
2 years ago
Wang yi

Babban jami’in diflomasiyyar kasar Sin ya bayyana a jiya Juma’a cewa, yana ziyara a kasar Amurka domin tattaunawa da bangaren Amurka kan aiwatar da muhimman matsaya da shugabannin kasashen biyu suka cimma, ta yadda za a tabbatar da daidaito da hana zaman lafiya tsakanin Sin da Amurka daga tabarbarewa, da dawo da alakarsu kan ingantaccen tafarkin ci gaba nan ba da jimawa ba. 

Wang Yi, mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar ya bayyana hakan ne yayin ganawa da shugaban kasar Amurka Joe Biden a birnin Washington D.C.

  • Bayan Nasara A Kotun Ƙoli, Tinubu Zai Ci Gaba Da Aikin Gina Nagartacciyar Ƙasa – Minista
  • CMG Ta Gabatar Da bukukuwan Baje Kolin Al’adun Sin Na Musamman A “Palace of Nations” Da Kasar Masar

Ya shaida wa Biden cewa manufar kasar Sin daya tilo a duniya da sanarwoyin hadin gwiwa guda uku tsakanin Sin da Amurka, su ne ginshikai mafi muhimmanci na dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, wadanda dole ne a kiyaye su ba tare da tsangwama ba.

Wang ya ce, “Ya kamata mu mutunta ka’idoji guda uku na mutunta juna, da zaman lafiya da samun moriyar juna da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar don daidaita dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.” Ya kara da cewa hakan ba wai kawai ya dace da muhimman muradun kasashen biyu da al’ummomin kasashen biyu ba ne, har ma da fatan al’ummar duniya baki daya.

Biden ya yi karin haske kan matsayinsa na dora muhimmanci kan dangantakar dake tsakanin Amurka da kasar Sin. Ya ce, Amurka a shirye take ta ci gaba da tuntubar kasar Sin, tare da tinkarar kalubalen duniya baki daya.

Shi Ministan harkokin wajen kasar Sin dai, yana ziyarar kwanaki uku a Amurka daga ranar 26 ga wata.

A lokacin da yake tattaunawa da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken, Wang Yi ya kuma yi kira da a samar da “Abubuwa biyar da suka zama dole” a dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka. Ya ce dole ne bangarorin biyu su kiyaye fahimtar juna da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da daidaita huldar dake tsakanin kasashen biyu, da barin hanyoyin sadarwa a bude, da daidaita bambance-bambance tsakanin kasashen biyu da sabani yadda ya kamata, kuma dole ne a inganta hadin gwiwar moriyar juna.

Wang Yi ya kuma gana da mai ba da shawara kan harkokin tsaro na kasar Amurka, Jake Sullivan, inda ya jaddada cewa, babban kalubale ga dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka shi ne “Yancin kai na Taiwan” .(Yahaya)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Fintiri A Matsayin Gwamnan Adamawa

Kotu Ta Tabbatar Da Zaben Fintiri A Matsayin Gwamnan Adamawa

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version