Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Shugaban Majalisar Dattawa Ya Sabunta Shaidar APC A Mazabarsa

by Muhammad
February 8, 2021
in LABARAI
2 min read
Shugaban Majalisa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela,

Shugaban majalisar dattawa ta Nijeriya, Sanata Ahmed Lawan ya sabunta shaidar jam’iyyar APC a mazabarsa da ke Gashuwa a jihar Yobe, ranar Asabar.

samndaads

A jawabin Sanata Lawan jim kadan da kammala cike takardar sabunta shaidar, ya bayyana cewa jam’iyyar APC ta gudanar da rijistar mambobinta karo na farko a 2014.

“Wanda tun daga wancan lokaci, akwai yan Nijeriya da damar gaske wadanda shekarun su suka kai 18 zuwa sama tare da burin shiga daya daga cikin jam’iyyun da muke dasu, sannan mafi yawa sun yanke shawarar kasancewa yan jam’iyyar APC, saboda haka wannan ita ce damar da zasu yi amfani da ita wajen yin rijista.”

Dr. Lawan ya kara da cewa, wanda kuma APC ta na kan yi wa sauran jam’iyyu zarra wajen kwashe babban kason sabbin mambobin masu rijistar a fadin kasar nan.

“Kuma hakan ya faru ne ta la’akari da dandazon jama’ar da ke canja sheka daga wasu jam’iyyu zuwa APC, wadanda kuma yanzu ne suke kokarin yin rijistar.”

Bugu da kari kuma, Lawan ya bayyana cewa aikin sabunta rijistar yana gudana wanda jam’iyyar APC ta na sa ran samun sabbin masu rijista sama da miliyan 100.

“Sannan kuma ta yadda aikin sabunta rijistar ke gudana, za a bai wa yan Nijeriya cikakkiyar damar fitowa domin sabunta yin rijistar, ba wai zai dakata a wannan wata ba ko makon farkon Maris ba.”

“Saboda haka za a yi amfani da wannan tsakani ne kawai domin gwaji tare da ayyana fara sabunta shaidar da rijistar sabbin mambobi. Mu na da burin yi wa akalla yan Nijeriya sama damiliyan 100 rijista.”

A hannu guda kuma, ya yi kira ga baki dayan yan jam’iyyar APC su nuna halaye nagari tare da biyayya da bayar da cikakken hadin kai a lokacin wannan aikin.

“Saboda wannan jam’iyya tamu ta na da isassun guraben da za ta jawo kowa da kowa a cikinta.” Ya bayyana.

SendShareTweetShare
Previous Post

Dole A Yi Garanbawul Wa AU Domin Cimma Manufofin Kungiyar, Cewar Buhari

Next Post

Cike Gurbi: Yadda Aka Gwabza Tsakanin Barayin Akwati Da Masu Kare Shi A Neja

RelatedPosts

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Gusau A shirin Gwamnatin Jihar Zamfara na...

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Mohammed, Matawallen...

Mun Soke Katin Shaidar Zama Dan Karamar Hukuma Kumbotso Saboda Bakin Haure – Garban Kauye

Mun Soke Katin Shaidar Zama Dan Karamar Hukuma Kumbotso Saboda Bakin Haure – Garban Kauye

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kano Shugaban karamar Hukumar Kumbotso Alhaji...

Next Post

Cike Gurbi: Yadda Aka Gwabza Tsakanin Barayin Akwati Da Masu Kare Shi A Neja

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version