Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Majalisar Dattawa Ya Sabunta Shaidar APC A Mazabarsa

by
1 year ago
in LABARAI
2 min read
Shugaban Majalisa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Maitela,

Shugaban majalisar dattawa ta Nijeriya, Sanata Ahmed Lawan ya sabunta shaidar jam’iyyar APC a mazabarsa da ke Gashuwa a jihar Yobe, ranar Asabar.

A jawabin Sanata Lawan jim kadan da kammala cike takardar sabunta shaidar, ya bayyana cewa jam’iyyar APC ta gudanar da rijistar mambobinta karo na farko a 2014.

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

“Wanda tun daga wancan lokaci, akwai yan Nijeriya da damar gaske wadanda shekarun su suka kai 18 zuwa sama tare da burin shiga daya daga cikin jam’iyyun da muke dasu, sannan mafi yawa sun yanke shawarar kasancewa yan jam’iyyar APC, saboda haka wannan ita ce damar da zasu yi amfani da ita wajen yin rijista.”

 

Dr. Lawan ya kara da cewa, wanda kuma APC ta na kan yi wa sauran jam’iyyu zarra wajen kwashe babban kason sabbin mambobin masu rijistar a fadin kasar nan.

“Kuma hakan ya faru ne ta la’akari da dandazon jama’ar da ke canja sheka daga wasu jam’iyyu zuwa APC, wadanda kuma yanzu ne suke kokarin yin rijistar.”

ADVERTISEMENT

Bugu da kari kuma, Lawan ya bayyana cewa aikin sabunta rijistar yana gudana wanda jam’iyyar APC ta na sa ran samun sabbin masu rijista sama da miliyan 100.

“Sannan kuma ta yadda aikin sabunta rijistar ke gudana, za a bai wa yan Nijeriya cikakkiyar damar fitowa domin sabunta yin rijistar, ba wai zai dakata a wannan wata ba ko makon farkon Maris ba.”

“Saboda haka za a yi amfani da wannan tsakani ne kawai domin gwaji tare da ayyana fara sabunta shaidar da rijistar sabbin mambobi. Mu na da burin yi wa akalla yan Nijeriya sama damiliyan 100 rijista.”

A hannu guda kuma, ya yi kira ga baki dayan yan jam’iyyar APC su nuna halaye nagari tare da biyayya da bayar da cikakken hadin kai a lokacin wannan aikin.

“Saboda wannan jam’iyya tamu ta na da isassun guraben da za ta jawo kowa da kowa a cikinta.” Ya bayyana.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Dole A Yi Garanbawul Wa AU Domin Cimma Manufofin Kungiyar, Cewar Buhari

Next Post

Cike Gurbi: Yadda Aka Gwabza Tsakanin Barayin Akwati Da Masu Kare Shi A Neja

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

by Leadership Hausa
4 hours ago
0

...

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

by Muhammad Bashir
6 hours ago
0

...

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

by Muhammad Bashir
15 hours ago
0

...

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

by
16 hours ago
0

...

Next Post

Cike Gurbi: Yadda Aka Gwabza Tsakanin Barayin Akwati Da Masu Kare Shi A Neja

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: