Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Shugaban Majalisar Dattawa Ya Taya Kiristoci murnar kirsimeti

by Muhammad
December 26, 2020
in RAHOTANNI
2 min read
Dattawa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela, Damaturu

 

samndaads

Shugaban majalisar dattawa a tarayyar Nijeriya, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan ya taya mabiya addinin kirista da daukacin al’umnar Nijeriya murnar zagayowar ranar da aka haifi Annabi Isah (as)- ranar bikin kirsimite ta 2020.

 

 

Baya ga hakan kuma, Sanata Lawan ya ce baya ga yadda Nijeriya ke fama da annobar korona, har wala yau Nijeriyw ta na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro da na matsin tattalin arziki.

 

Bugu da kari kuma, ya ce duk da wannan mawuyacin halin da ake ciki, ya ce akwai kwarin gwiwa matukar yan kasa su ka jajirce ta hanyyar hadin kai da fahimtar juna, kishin kasa ta aiki tukuru wajen ci gaban Nijeriya.

A hannu guda kuma, shugaban majalisar ya bukaci mabiya addinin kirita su yi amfani da wadannan ranaku wajen yi wa Nijeriya addu’a ta musamman ga shugabanni a kokarin samun nasarar magance matsalolin tsaro da bunkasar tattalin arziki.

“Saboda haka ina taya mabiya addinin kirista murnar zagayowar wannan muhimmiyar rana wadda makamancinta aka haifi Yesu Kiristi”

“Ya kamata mu yi amfani da wannan lokaci wajen nuna soyayyar mu ga makwabta, tausaya wa ga masu karfin karfi da marasa galihu, mu yi hakuri da juna ba tare da la’akari da bambancin addini, siyasa ko kabilanci ba, saboda tuna wa da rayuwar Yesu Christi mai cike da sadaukarwa da jinkai ga duniya baki daya.”

Shugaban majalisar ya ce bisa ga yadda annobar korona ta sake dawowa gadan-gadan, ya zama wajibi yan Nijeriya su daura damara wajen bin ka’idojin da hukumomi suka gindaya.

Haka zalika kuma, Lawan ya yaba wa kwamitin shugaban kasa kan annobar dangane da kokarin da suke yi na ci gaba da wayar da kan yan Nijeriya bisa ga yanayin cutar, sannan kuma ya yaba wa ma’aikatan lafiya bisa yadda su ke gudanar da yaki da cutar.

Sanata Lawan ya kara da cewa zauren majalisar dattawan ya na tattauna wa da hukumomin da al’amarin ya shafa wajen ganin an bi ka’idojin da su ka dace a kokarin da gwamnatin Nijeriya ke yi wajen sayo wa da rarraba allurar riga-kafin cutar korona, tare da tabbatar da cewa an yi wa kowane dan Nijeriya riga-kafin.

SendShareTweetShare
Previous Post

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Kame Dan Bindigar Da Ya Kashe Dan Kasar Jamus

Next Post

Gwamnatin Gombe Ta Fara Biyan Diyyar Wadanda Aikin Kafa Sansanin Masana’antu Ya Shafa

RelatedPosts

Ta’aziyar Rasuwar Sam Nda Isaiah

Sam Nda-Isaiah Ya Rasu Lokacin Da Ake Tsananin Bukatar Gudunmawarsa – Jami’ar Jos

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Shugabannin jami’ar Jos sun bayyana rashin jin dadinsu dangane da...

Kasuwar Mile 12

Kwamitin Da Shugaban Kasuwar Mile 12 Ya Nada Na Cigaba Da Jajanta Wa Manoman Arewacin Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Sabon kwamitin da Babban Shugaban kasuwar mile 12 Intanashinal market...

Sojoji Sun Farmaki Mahakar Ma’adanai A Zamfara, Sun Cafke ‘Yan Bindiga 150

Ranar Mazan Jiya: Babu Wani Abin Murna Ga Tabarabrewar Tsaro – Dattawa Ga Buhari

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Dattawan Nijeriya a karkashin inuwar gamayyar kungiyar wato (COPANE), sun...

Next Post
Sansanin

Gwamnatin Gombe Ta Fara Biyan Diyyar Wadanda Aikin Kafa Sansanin Masana'antu Ya Shafa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version