CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Shugaban Nijeriya Ya Tattauna Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Kan Dangantakar Kasashen Biyu

by CRI Hausa
January 6, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Shugaban Nijeriya Ya Tattauna Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Kan Dangantakar Kasashen Biyu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, ya gana da mamban majalisar gudanarwar kasar Sin kuma ministan harkokin kasar Wang Yi, wanda ke ziyara a kasar, inda dukkansu suka yi alkawarin inganta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu a dukkan fannoni.
Muhammadu Buhari, ya ce cikin sama da shekaru 50 da suka gabata, dangantakar Sin da Nijeriya ta haifar da muhimman sakamako.
Ya ce a lokacin da farashin mai ya fadi, Nijeriya kuma ke fuskantar matsalolin ci gaba, tallafin Sin ya taimaka mata, domin ta shawo kan matsalolin da suka hada da rashin kayayyakin more rayuwa da karancin abinci, yana mai cewa, Sin ta taka gagarumar rawa a fannin ci gaban kasar.
A nasa bangaren, Wang Yi, ya ce a matsayinta na babbar kasa a nahiyar Afrika, Nijeriya ta dauki wani muhimmin matsayi a bangaren dangantakar diflomasiyyar Sin da nahiyar Afrika. Ya ce abu mafi muhimmanci a dangantakar kasashen biyu cikin shekaru 50 da kulla ta shi ne, fahimta da aminci da goyon bayan juna.
Ya ce a shirye Sin take ta hada hannu da Nijeriya wajen daukaka huldar kasa da kasa da inganta tsarin demokradiyya a dangantakar kasashen duniya da kare halaltattun hakkoki da muradun kasashen biyu da ma na sauran kasashe masu tasowa. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

SendShareTweetShare
Previous Post

Rushe Gidan Abinci: Gwamnatin Kaduna Ta Bayyana Dalilanta

Next Post

Kyakkyawar Jumma’a Tun Daga Laraba Ake Gane Ta

RelatedPosts

Sanya Takunkumi Kan Pompeo Da Sauran Wasu Amurkawa 27 Abu Ne Da Ya Dace

Sanya Takunkumi Kan Pompeo Da Sauran Wasu Amurkawa 27 Abu Ne Da Ya Dace

by CRI Hausa
3 hours ago
0

Kwanan nan, gwamnatin kasar Sin ta sanar da sanya takunkumi...

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Ketare A Shekarar 2020 Ya Karu Da 3.3%

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Ketare A Shekarar 2020 Ya Karu Da 3.3%

by CRI Hausa
3 hours ago
0

Kididdigar da ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin da hukumar kula...

Xi Ya Jaddada Muhimmancin Aiki Da Dokokin Jam’iyya A Lokacin Aiwatar Da Ajandar Raya Kasa Ta Shekaru 5 Karo Na 14

Xi Ya Jaddada Muhimmancin Aiki Da Dokokin Jam’iyya A Lokacin Aiwatar Da Ajandar Raya Kasa Ta Shekaru 5 Karo Na 14

by CRI Hausa
3 hours ago
0

Shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi...

Next Post
Kyakkyawar Jumma’a Tun Daga Laraba Ake Gane Ta

Kyakkyawar Jumma’a Tun Daga Laraba Ake Gane Ta

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version