Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Shugaban NIS Babandede Ya Bayyana Alhinin Rasuwar Janar Attahiru Da Sauran Dakaru  

by
12 months ago
in LABARAI
2 min read
Shugaban NIS Babandede Ya Bayyana Alhinin Rasuwar Janar Attahiru Da Sauran Dakaru   
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta ƙasa (NIS), CGI Muhammad Babandede ya bayyana alhinin rasuwar Babban Hafsan Sojojin ƙasa,Laftanar Janar Ibrahim Attahiru da sauran hafsoshi da matuƙa jirgin da ya yi hatsari da su, tare da miƙa ta’aziyyarsa ga Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari da sauran iyalan marigayan waɗanda ya ce sun riga mu gidan gaskiya ne yayin da suke aiki na kishin ƙasa.

CGI Babandede ya bayyana rasuwar babban hafsan sojin da sauran hafsoshin da ke tare da shi a matsayin babban giɓi ga ƙasa, wanda ya ce ya zama wajibi a cike domin ci gaba da yaƙi da matsalar tsaro da sauran miyagun laifukan da ke barazana ga zaman lafiyar ƙasar nan.

Shugaban Hukumar NIS, Muhammad Babandede

Shugaban na NIS ya ce marigayan sun nuna kishin ƙasa ta hanyar sadaukarwa wanda a kai ne suka riga mu gidan gaskiya, yana mai ƙarawa da cewa, “Babban Hafsan Sojin jarumi ne na gaske, ya kasance ɗaya daga cikin mafi ƙwarewa a tsakanin manyan hafsoshin sojin ƙasar nan a wannan zamanin. Yana aiki cikin ƙwarin gwiwa da ɗa’a da nuna ƙwarewa da kuma kishin ƙasa”

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama na NIS, CIS Sunday James ta ruwaito CGI Babandede yana kwatanta rasuwar babban hafsan sojin a matsayin mai raɗaɗi bisa la’akari da manyan jami’an da ke tare da shi masu ɗa’a cikin ayyukansu waɗanda hatsarin ya rutsa da su. Bugu da ƙari, ya ce a fili yake cewa babban hafsan da sauran manyan jami’an sun tafi sun bar ƙasar da suke matuƙar ƙauna a daidai lokacin da aka fi buƙatar aiki da ƙwarewa da basirar da suke da su na aiki.

CGI Babandede ya yi kira ga dakarun sojin ƙasar nan manya da ƙanana kar su bari babban rashin da aka yi ya danƙwafar da su, maimakon haka su ƙara mayar da hankali wurin nuna gwarzantaka a yaƙin da ake yi tare da kammalawa cikin ƙanƙanin lokaci a matsayin hanyar jinjina wa sadaukarwar da babban hafsan ya yi, da cika burinsa na maido da doka da oda a ƙasar nan. Ya ce wannan ita ce babbar hanyar karrama shi da kuma tunawa da shi da sauran mazan jiya da suka riga mu gidan gaskiya.

 

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Ya Bukaci Makota Su Ci Gaba Da Ba Da Gudummowa Kan Tsaro A Jami’ar Ahnadu Bello

Next Post

Karamar Hukumar Toungo A Adamawa Ta Samu Wutar Lantarki Bayan Tsawon Shekara 25

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

by
3 hours ago
0

...

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

by
15 hours ago
0

...

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

by Abdulrazaq Yahuza Jere
24 hours ago
0

...

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

by Abubakar Abba
2 days ago
0

...

Next Post
Gwamnatin Masar

Karamar Hukumar Toungo A Adamawa Ta Samu Wutar Lantarki Bayan Tsawon Shekara 25

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
 

Loading Comments...
 

    %d bloggers like this: