Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Ƙarin Girma Ga Jami'ai 4,526
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Ƙarin Girma Ga Jami’ai 4,526

byyahuzajere
3 years ago
NIS
Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa, Isah Jere Idris ya sanar da ƙarin girma ga jami’an hukumar su 4,526 da suka yi jarrabawar ƙarin girma da waɗanda suka samu horaswa daban-daban ta ɗaga darajar muƙami a shekarar 2021.
  • “Ba Zan Mara Wa Atiku Ko Wani Dan Takara Na Kyale Tinubu Ba” —Buhari
Tabbatar da ƙarin girman na ƙunshe ne a cikin wasiƙar da ta zo daga Hukumar Gudanarwar Rundunonin da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Cikin Gida da aka yi wa lambar CDCFIB/S.33/VOLIII/54 mai ɗauke da kwanan wata,18 ga Agusta, 2022.
NIS
Shugaban hukumar ya bayyana hakan ne a yau a hedikwatarta yayin da yake yi wa wasu jami’ai masu taimaka masa  da ke cikin ma’aikatan da aka yi wa ƙarin girma ado da sabbin muƙamansu.
NIS
Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulɗa da jama’a na NIS, wanda shi ma aka ƙara masa girma daga ƙaramin Mataimakin Kwanturola (ACI) zuwa Babban Mataimakin kwanturola (DCI), Amos Okpu, ta ce jami’ai masu muƙamin ƙaramin mataimakan Kwanturola 145 sun samu ƙarin girma zuwa Babban Mataimakin Kwanturolan Shige da Fice; sannan masu muƙamin Babban Sufiritanda 99 sun samu ƙarin girma zuwa ƙaramin mataimakin Kwanturola.
Bugu da ƙari, akwai masu muƙamin Sufiritanda 307 da aka mayar da su matsayin Babban Sufiritanda; kana mataimakan Sufiritanda 338 sun samu ci gaba zuwa matsayin Sufiritanda.
NIS
Sauran waɗanda suka samu ƙarin girman su ne jami’ai 589 da aka ciyar da su gaba zuwa muƙamin mataimakin Sufiritanda na ɗaya (I), sai wasu  794 da aka ƙara musu muƙami zuwa Mataimakan Sufiritanda na biyu (II).
Har ila yau takardar ta yi bayanin cewa,
jami’ai masu muƙamin Sufeto 21 sun samu ci gaba zuwa mataimakin Sufiritanda na biyu (II). Yayin da wasu jami’ai 1254 suka sami ci gaba zuwa matsayi na Mataimakin Sufeto na biyu (II), kana akwai jimillar ƙananan jami’ai 979 da suka samu ƙwarewar aiki da aka ɗaga darajarsu zuwa matsayi na Mataimakin Sufiritanda na biyu.
NIS
Da yake jawabi a wajen bikin adonta muƙarrabansa, Shugaban NIS CGI Isah Jere Idris ya yaba wa Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola wanda kuma ya zama shugaban hukumar gudanarwar rundunonin da ke ƙarƙashin ma’aikatar bisa jajircewarsa wajen ciyar da ma’aikata gaba.
Ya bukaci sabbin jami’an da aka kara musu girma da su ƙara ƙwazo da saka karamcin da aka yi musu ta hanyar sadaukarwa da kuma biyayya a bakin aiki.
Ya kuma bai wa gwamnati tabbacin cewa hukumar a ƙarƙashinsa za ta ci gaba da bayar da gudunmawa mai amfani ga zaman lafiya da ci gaban kasa.
NIS
Daga cikin jami’an da aka yi wa ado da sabbin mukamansu akwai Jami’in hulɗa da jama’a na NIS Amos OKPU, wanda aka ƙara wa girma zuwa DCI; da Jami’in kula da tsare-tsare na Kwanturola Janar MY Dutse mai barin gado da magajinsa MA Ajimobi wanda a yanzu suka zama Manyan Mataimakan Kwanturola.
NIS
Sauran sun haɗa da Mercy Gadzama, Manajar Kula da Cibiyar Fasaha ta NIS, da a yanzu ta zama Babbar Sufiritanda, da Jami’in Tsaro na Kwanturola Janar AO Olukoya, da aka kara masa girma zuwa muƙamin Babban Sufiritanda da Tanko Godiya da Nguar Loice Titus na Sashen Kai Ɗaukin Gaggawa (RRS), duka biyu da aka ƙara musu girma zuwa mataimakan Sufiritanda na Shige da Fice (II).
ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
kenya

Darussa Ga Nijeriya Daga Zaben Kasar Kenya

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version