Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Shugabannin Arewa Sun Shawarci Al’ummansu Mazauna Kudu

by Tayo Adelaja
September 26, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga A.A. Masagala, Benin.

A cikin wannan makon ne shugabannin ‘yan Arewa mazauna yankin Kudancin kasar nan suka bayyana bukatar cewa, ‘yan Arewa da suke zirga-zirga a Kudu da su kasance tsintsiya madaurinki guda a cikin harkokinsu na yau da kullum.

samndaads

Shugabannin da suka hada da; Alhaji Badamasi Saleh jagoran alummar Arewa mazauna garin Benin, ya yi kira tare da shawartar alummar Arewar na jihohin Kudu a kan zaman lafiya da hadin kai. Yana mai cewa, “Ya kamata kowa ya sani zaman lafiya shi ne tushen arziki na alummar kasa, don haka wajibi ne mu tabbatar da shi a tsakaninmu kafin mu kawo komai mu dora sannan mu kasance mun hada kai da shugabanninmu kana mu guji aikata munanan dabi’u.”

Haka nan ya ce duk dan Arewa mazaunin Kudu ya kasance yana mutunta kansa ya siffantu da mutane na kwarai kuma ya nesanta kansa daga neman rikici. Tare da yin kira ga shugabannin Arewa da su tashi tsaye su ci gaba da fadakar da matasansu da sauran jama’a game da muhimmancin zaman lafiya.

Shi ma a nasa bangaren, Alhaji Sani Idiris Sani wanda shi ne sarkin Nufawa na Jihar Edo, shawar ce  ya bayar inda ya ce, “Wajibi ne mu kasance masu hakuri da junanmu da kuma sauran abokan zamanmu, mu yi zama  na ‘yan uwantaka kuma mu bar  yin amfani da shaci-fadi da yada jita-jita a kan abin da bai tabbata ba domin yin hakan yana kawo rudani da tashin hankali a tsakanin jama’a, don haka ya kamata mutane masu aikata irin wadannan miyagun dabi’un su daina, sannan mu ci gaba da zama da junanmu lafiya”.

SendShareTweetShare
Previous Post

Hukumar NDLEA Ta Nemi Hadin Kan Al’umma A Kano

Next Post

Ilimi Jigo Ne Na Yakar Talauci –Masari

RelatedPosts

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
7 hours ago
0

Kamar dai yadda aka sani kananan hukumomi sune suka kasance...

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Canja Shugabannin Tsaron Nijeriya

’Yan Yankin Arewa Maso Gabas Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Kan Sauke Shugabannin Tsaro

by Sulaiman Ibrahim
7 hours ago
0

Biyo bayan sauke shugabannin tsaron Nijeriya tare da nada sababbi...

Ya Kashe Mata Da Yaro Da Shebur

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

A yau aka kama wani mutum mai shekaru 28, Chukwuemeka...

Next Post

Ilimi Jigo Ne Na Yakar Talauci –Masari

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version