Shugabannin Sin Da Rasha Sun Yi Taron Manema Labarai Na Hadin Gwiwa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Sin Da Rasha Sun Yi Taron Manema Labarai Na Hadin Gwiwa

byCGTN Hausa
1 year ago
Sin

A yau Alhamis shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin sun gudanar da taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Beijing.

A yayin taron, shugaba Xi ya jaddada cewa, a bana ake cika shekaru 75 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Rasha. Kuma dangantakar sassan biyu ta zamo muhimmin misali na sabon salon alakar kasa da kasa, da kuma kyakkyawan kawancen manyan kasashe biyu dake makwaftaka da juna. Ya ce, ci gaban bunkasar alakar sassan biyu, na da nasaba da yadda suke dora muhimmanci ga ka’idoji 5.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace 130 A Zamfara
  • Amurka Za Ta Lashe Amanta Game Da Karin Harajin Rashin Adalci Da Ta Bugawa Kasar Sin

Na farko, shugaba Xi ya ce, Sin da Rasha, na dora muhimmanci ga martaba juna a matsayin jigon alakarsu, kuma har kullum suna goyon bayan juna wajen kare manyan muradunsu. Na biyu kuma, sassan biyu suna rungumar hadin gwiwar cimma moriyar juna, a matsayin karfin dake ingiza kawancensu, da aiki wajen yaukaka sabon salon cimma moriya tare. Na uku kuma, Sin da Rasha na kara azamar wanzar da abota a matsayin tushen dangantakarsu, da ingiza kawancensu zuwa mataki na gaba. Na hudu kuma, kasashen biyu na rungume da manufar kyautata tsare-tsare bisa matsayin koli, a matsayin hanyar tabbatar da kawance, da karkata akalar jagorancin duniya zuwa turba ta gari. Na biyar kuma, Sin da Rasha sun himmantu wajen tabbatar da daidaito, da adalci, a matsayin dalilin bunkasa alakokinsu, da mayar da hankali ga warware batutuwa masu jan hankali ta hanyar siyasa.

Sannan a yau shugaban kasar Sin Xi Jinping, da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin sun halarci bikin kaddamar da shekarar al’adun Sin da Rasha, da bikin kide-kide da raye-raye na musamman, wanda aka shirya a birnin Beijing, domin murna cika shekaru 75 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Rasha.

A bana, sassan biyu na Sin da Rasha za su gudanar da ayyukan musayar al’adu masu kayatarwa, don zurfafa hadin gwiwar musayar al’adunsu, da aiki tare, wajen bude sabon babin ingiza musayar al’adu tsakanin Sin da Rasha.

Bugu da kari, a yau Alhamis, shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Rasha Vladimir Putin sun sa hannu, da kuma gabatar da wata hadaddiyar sanarwa, game da karfafa dangantakar abokantakar hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a sabon zamani tsakanin jamhuriyar jama’ar kasar Sin da tarayyar Rasha, yayin da ake cika shekaru 75 da kulla huldar diplomasiyya tsakanin kasahsen biyu. (Saminu Alhassan, Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi

Sin: Karbuwar Hajojin Sin Masu Nasaba Da Sabbin Makamashi Ba Shi Da Nasaba Da Samar Da Tallafi

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version