Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Shugabar Jami’ar FUGA Ta Bukaci ‘Yan Kwangila Su Hanzarta Kammala Ayyukan Su

by Muhammad
April 3, 2021
in LABARAI
1 min read
Shugabar Jami’ar FUGA Ta Bukaci ‘Yan Kwangila Su Hanzarta Kammala Ayyukan Su
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela,

Shugabar jami’ar gwamnatin tarayya da ke Gashuwa jihar Yobe (FUGA), Farfesa Maimuna Waziri, ta yi kira ga yan kwangilar da aka bai wa kwangilar ayyuka a jami’ar su gaggauta kammala su ba tare da bata lokaci ba.

Shugabar jami’ar ta yi wannan kira a sa’ilin da tawagar yan kwangila tare da masu sanya ido kan ayyukan su ka kai mata ziyarar ban girma a ofishin ta ranar Laraba.

A nashi jawabin, jagoran tawagar, Architect Abdullahi Sa’id Bello, ya bayyana cewa sun kai ziyarar ne don taya Farfesa Maimuna Waziri murnar nadata a matsayin shugabar jami’ar ta uku tare da samun damar tattauna wa da manyan jami’an jami’ar. Wanda Architect Abdullahi ya kara da cewa, ayyukan guda shidda ne wadanda yan kwangila daban-daban ke tafiyar dasu ba tare da wata matsala ba.

A hannu guda kuma, ya ce duk da hakan akwai yan wasu yan takaddamar da suka shiga tsakanin yan kwangilar da masu kula da ayyukan dangane da inganci da wasu yan bayanai a matsayin wasu daga cikin dalilan da suka kawo tsaikon da ya sa har yanzu ba a kammala su ba. Wanda bisa ga hakan ya bukaci jami’ar ta taimaka ta saka baki wajen kara lolacin da aka kayyade na wasu watanni don samun damar kammala wa bisa ka’ida.

A nashi bangaren, rijistaran jami’ar FUGA, Dr. Aliyu Bulkaciwa Shehu, ya bayyana godiyar sa ga tawagar yan kwangilar dangane da daukar lokacin su domin kawo wa jami’ar ziyara da neman hadin kai.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Yi Wa Fiye Da Mutum 15,000 Rigakafin Korona Cikin Kwanaki 7 A Jihar Gombe

Next Post

Batan Jirgin Yaki: Shugaban Rundunar Sojan Sama Ya Ziyarci Borno 

RelatedPosts

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Zirin Gaza

by Sulaiman Ibrahim
9 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Isra'ila ta ce ta kai harin bama-bamai...

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

Yadda Sojoji Suka Kashe Kwamandan ISWAP A Damasak

by Sulaiman Ibrahim
9 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Wani babban kwamandan ISWAP, Bukar Gana (wanda...

NDLEA

NDLEA Ta Sanar Da Fara Kai Farmaki Dakunan Hada Muggan Kwayoyi

by Muhammad
14 hours ago
0

Daga Bello Hamza, Shugaban hukuamar NDLEA Birgediya Janar Buba Marwa...

Next Post
Batan Jirgin Yaki: Shugaban Rundunar Sojan Sama Ya Ziyarci Borno 

Batan Jirgin Yaki: Shugaban Rundunar Sojan Sama Ya Ziyarci Borno 

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version