Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

(Sickbay) Na Jami’ar Ahmadu Bello Zariya Ya Zama Cikakken Asibiti

by Tayo Adelaja
August 11, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Idris Umar, Zariya.

A kwanakin baya ne shugaban jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Farfesa Ibrahim Garba ya jagoranci bikin bude sabuwar cibiyar kula da lafiyar dalubai da ma’aikata wanda ke a cikin harabar jami’ar.

samndaads

A yayin da ya ke jawabi a wajen taron ya ce, “Cibiyar an samar da ita ne a sakamakon bukatar da jami’ar ke da ita na samar da ingantaccen wajen kula da lafiya.” Farfesa ya kara da cewa, “Cibiyar lafiyar ita ta maye gurbin wajen kula da lafiyar jami’ar na da wanda aka fi sani da suna (Sick bay), wanda a baya ba komai da ake bukata ya ke da shi ba, amma yanzun kuwa ya zama sabuwar cibiyar mai dauke da duk wani abu na kula da lafiya da ake bukata a manyan asibitocin da ke fadin kasar nan.”

Har wa yau shugaban jami’ar ya bayyana cewa cibiyar wata dama ce ga sababbin likitocin da aka turo cibiyar kula da lafiyar domin koyon aikin likitanci, don haka sai ya bukaci hukumar kula da cibiyar da su dage wajen ganin an cimma manufar kaukaka wajen.

Daraktar ta kara da cewa cibiyar tana samar da duk wasu manyan harkokin kula da lafiya kuma ta samu shaida daga hukumar NIHS, don haka ne tayi kira ga mazauna kusa da asibitin da su nuna kauna ga asibitin wanda hakan zai sanya shi asibitin ya samu cigaba mai dorewa, kuma tayi kira da bubban murya da cewa duk wanda yake son bayar da wata gudummawa ta kowani sashi to cibiyar a shirye take ta karbi gudummawar, a karshe ne tayi yabo ga shugaban jami’ar Farfesa Ibrahim Garba bisa ga irin gudummawar da yake bayarwa a fannoni daban-daban wanda hakan ke sa lamarin kiwon lafiya ke bunkasa a  jami’ar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Harin Paris: ‘Yan Sanda Sun Harbe Direban Motar Da Ake Zargi Da Afkama Sojoji

Next Post

Ziyarar Sarkin Kano A Kasar Sin

RelatedPosts

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

by Sulaiman Ibrahim
11 hours ago
0

Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin da aka diba wa ’yan...

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

by Sulaiman Ibrahim
11 hours ago
0

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, ayau Juma’a, ta ce shirin Gwamnatin...

Zakzaky

Matar Sheikh EL-Zakzaky Ta Kamu Da Korona, In Ji Danta

by Muhammad
16 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Matar Shugaban Kungiyar Musulunci a Nijeriya...

Next Post

Ziyarar Sarkin Kano A Kasar Sin

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version