CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Sin Da Masar Sun Rattaba Hannu Kan Takardar Hadin-Gwiwa Kan Allurar Riga-Kafin Annobar COVID-19

by CRI Hausa
January 1, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Sin Da Masar Sun Rattaba Hannu Kan Takardar Hadin-Gwiwa Kan Allurar Riga-Kafin Annobar COVID-19
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ranar 31 ga watan Disambar shekara ta 2020, jakadan kasar Sin dake kasar Masar Liao Liqiang ya rattaba hannu tare da mataimakin ministan kula da lafiya da harkokin alumma na kasar Mohamed Hassani, kan takardar hadin-gwiwar kasashen biyu game da allurar riga-kafin annobar COVID-19. Mista Liao ya kuma gana da ministan kula da lafiya da harkokin alumma na Masar Hala Zayed.

Jakada Liao ya ce, takardar da aka daddale tsakanin kasashen biyu, za ta sa kaimi ga hadin-gwiwarsu a fannonin da suka shafi nazari da samarwa gami da amfani da allurar riga-kafin annobar COVID-19, ya kuma ce, cutar ba ta san iyakokin kasa da kasa ba, kana, daukacin alummun kasa da kasa suna da hakkin samun allurar riga-kafi gami da maganin cutar.
A nasa bangare, Hala Zayed ya ce, gwamnati gami da kamfanonin kasar Sin duk suna himmatuwa, wajen samar da goyon-baya da babban tallafi ga kasar Masar don dakile annobar, abun da ya cancanci babban yabo gami da matukar godiya.
Ya kara da cewa, an yi nasarar gudanar da gwaje-gwaje kan allurar riga-kafin da kamfanin harhada magunguna na kasar Sin ko kuma SINOPHARM a takaice ya samar, kuma an tabbatar da inganci gami da tasirin riga-kafin. Masar tana fatan hada kai tare da kasar Sin a fannin samar da allurar riga-kafin cutar COVID-19, da ci gaba da samun goyon-baya daga kasar ta Sin. (Mai Fassara: Murtala Zhang)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Kasar Sin Tana Taimakawa Ci Gaban Duk Duniya

Next Post

Yadda Cin Zarafi Ke Neman Zama Dabi’ar Wasu ‘Ya’yan Jam’iyyar APC Ta Jihar Kano

RelatedPosts

Allurar Rigakafin Da Sin Ta Samar Na Da Inganci

Allurar Rigakafin Da Sin Ta Samar Na Da Inganci

by CRI Hausa
6 hours ago
0

Ran 30 ga watan Disamba na shekarar bara, bayan allurar...

Rikicin Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Ya Jawo Asarar Guraben Ayyuka 245,000 A Amurka

Rikicin Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Ya Jawo Asarar Guraben Ayyuka 245,000 A Amurka

by CRI Hausa
10 hours ago
0

Wani nazari da cibiyar binciken harkokin tattalin arziki ta Oxford...

Amurka Za Ta Yi Wa Kanta Illa, Idan Ta Ci Gaba Da Hana Hajojin Jihar Xinjiang Shiga Kasar

Amurka Za Ta Yi Wa Kanta Illa, Idan Ta Ci Gaba Da Hana Hajojin Jihar Xinjiang Shiga Kasar

by CRI Hausa
11 hours ago
0

kwanan nan, hukumar kwastan da hukumar kare iyakokin Amurka, sun...

Next Post
Yadda Cin Zarafi Ke Neman Zama Dabi’ar Wasu ‘Ya’yan Jam’iyyar APC Ta Jihar Kano

Yadda Cin Zarafi Ke Neman Zama Dabi'ar Wasu 'Ya'yan Jam'iyyar APC Ta Jihar Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version