Sin Ta Baiwa Duk Duniya Sako Mai Yakini
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Baiwa Duk Duniya Sako Mai Yakini

byCGTN Hausa
2 years ago
Sin

Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya amsa tambayoyin da ’yan jarida na gida da waje suka yi masa, a gun taron manema labarai da aka gudanar kan manyan taruka biyu wato na NPC da CPPCC, wadanda suka shafi huldar kasa da kasa da abubuwa masu jan hankalin mutane da daidaita harkokin duniya da sauransu. Amsoshin da ministan ya bayar dangane da tambayoyin da aka yi masa, sun baiwa duk fadin duniya sako mai yakini cewa, Sin tana taka rawar gani a duniya bisa bunkasuwarta mai karko.

“Sin za ta nace ga matsayin kasancewar karfi mai karko wajen ciyar da zaman lafiya da ci gaban duniya gaba”, kafofin yada labarai na kasa da kasa sun mai da wannan magana matsayin da Sin take dauka ta fuskar diplomasiyya.

  • Ba Za Mu Lamunci Cin Zarafin Wani Da Sunan Tafsiri Ba – Gwamnatin Kaduna
  • Wasoso Da Fasa Rumbunan Hatsi Ba Za Su Magance Yunwa Ba – Farfesa Sanda

A halin yanzu, ana ci gaba da fama da rikicin Ukraine, baya ga rikicin Palasdinu da Isar’ila dake kara tsananta, kuma siyasar yankuna na kara kamari. Ba fatan tabbatar da tsaro da zaman lafiya cikin kasarta kadai Sin ke yi ba, har ma da son taka rawa wajen samar da zaman lafiya a duk duniya

A gun taron manema labarai, Sin ta gabatar da wata hanya mai salon kasar wajen magance matsalolin dake jan hankalin mutane, wato nacewa ga hana tsoma baki cikin harkokin gidan sauran kasashe, da warware rikici a siyasance bisa adalci da daidaito, ta yadda za a daidaita batutuwa daga tushe.

Manufar da Sin take dauka wajen magance harkokin duniya ita ce, gudanar da harkokin duniya tsakanin bangarori daban-daban cikin adalci bisa oda da doka, da samun ci gaban tattalin arzikin duniya tare bisa ka’idar hakuri da juna, matakin da ya dace da halin da ake ciki, kuma ya bayyana muradun kasashe masu tasowa baki daya.

Kazalika, duniya na fama da karancin karfin samun bunkasuwa, kana wasu kasashe na daukar matakin katse hulda, game da hakan, Sin ta bayyana matsayin da ta kan dauka cewa, dole ne a kafa tsarin tattalin arziki mai bude kofa.

Bugu da kari, a shekarar bara, yawan bunkasuwar Sin ya kai kashi 5.2%, wanda ya taka rawa na kashi 1/3 ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya, hakan ya sa Sin take taka rawar gani wajen ingiza bunkasuwar duniya.

Yanzu, duniya na shiga wani yanayi mai cike da mabambantan sauye-sauye, jama’ar duniya na ganin muhimmancin kafa kyakkyawar makomar Bil Adama ta bai daya, da fahimtar rawa mai dorewa da Sin take bayarwa. A lokacin bazarar bana, wadannan manyan taruka biyu na fitar da sako mai yakini ga duk fadin duniya cewa, Sin za ta ci gaba da ingiza bunkasuwar duniya mai dorewa ba tare da sauyawa ba. (Amina Xu)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Next Post
Kasar sin

Kasar Sin Ta Gano Filin Hakar Mai Na Farko A Ruwa Mai Zurfi Mai Yawan Ton Miliyan 100

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version